Aminiya:
2025-05-28@11:43:27 GMT

An shiga nuna wa juna yatsa tsakanin Hamas da Isra’ila

Published: 10th, February 2025 GMT

Hamas ta sanar da yanke shawarar jinkirta sakin fursunonin Isra’ila nan gaba har sai abin da hali ya yi.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da ƙungiyar gwagwarmaya ta Falasɗinu ta fitar tana mai cewa an ɗauki matakin ne a matsayin mayar da martani ga keta yarjejeniyar tsagaita wuta da Isra’ila ta yi.

Dalilin da na ziyarci Obasanjo — Atiku Gwamnan Zamfara ya gindaya sharaɗin sulhu da ’yan bindiga

Sanarwar da ɓangaren sojin Hamas ɗin ya fitar ta ce “fiye da mako uku, shugabacin ƙungiyar na bibiyar yadda maƙiya suka gaza cika ka’idojin yarjejeniyar da suka cimma.

“Karya wannan ƙa’ida, har da jinkirta dawowar waɗanda suka rasa muhallansu zuwa Arewacin Gaza, inda ake fakon su tare da harbin su, da harba musu bama-bamai, a yankuna daban-daban na Gaza, wanda hakan ke nuni da yadda suka gaza ƙyale ayyukan jinƙai, da sauran yarjejeniyar da suka cimma tunda farko.

“Baya ga nan, dakarun na Hamas tun farko sun mutunta wannan alƙawari da aka yi.

Saboda haka Hamas ta ce “sakin ƙarin wasu masu rajin kafa ƙasar Yahudawa a ranar Asabar, 25 ga watan 2025, sun dakatar da shi, sai nan gaba, yayin da suke jiran maƙiya, za su fara mutunta yarjejeniyar da aka cimma da aka fara aiwatarwa makonin da suka gabata.

“Muna sake jadada aniyarmu ta ci gaba da mutunta dukkan yarjejeniya da ka’idojin da aka gindaya, idan har masu mamayar suka bi su sau da ƙafa.

A shirye muke mu ɗauki mataki — Isra’ila

Tuni ita ma Isra’ila ta mayar da martani dangane da sanarwar da Hamas ta fitar ta dakatar da sakin mutanen da take garkuwa da su.

Sanarwa da Ministan Tsaron Isra’ila ya fitar ta ce “sanarwar dakatar da sakin waɗanda Hamas ke garkuwa da su ya saɓa yarjejeniyar tsagaita cimma wutar da ta musayar fursunoni da aka amince,” in ji Israel Katz.

“Na bai wa dakarun IDF umarnin kasancewa cikin shirin ko-ta-kwana dangane da duk wani da ka iya biyo ba a Gaza domin kare al’umma.

“Ba za mu bari a maimaimata abin da ya faru ranar 7 ga watan Oktoba ba..” in ji Katz.

Wannan dai na zuwa ne a yayin da yarjejeniyar tsagaita wuta a yaƙin da Isra’ila ke yi a Gaza ta shiga kwana na 23 a yau Litinin.

Rahotanni sun ce yaƙin ya kashe fiye da Falasɗinawa 48,180, inda a yanzu aka sauya alƙaluman zuwa 62,000 saboda an ayyana waɗanda suka ɓata a matsayin matattu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Falasɗinawa Isra ila

এছাড়াও পড়ুন:

Rikici Ya Ɓarke Tsakanin ‘Yansanda Da Matasa A Rano, Mutum 1 Ya Mutu, An Harbi Wasu

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tashin Hankali A Gaza Bayanda HKI Ta Bude Rumbun Ajiyar Kayakin Agaji A Rafah
  • Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Nuna Misali Na Bude Kofa Da Raya Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da ASEAN Da GCC
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Ce: Dole Ne A  Dauki Kwararan Matakan Don Dakatar Da Laifukan Gaza
  • CMG Ta Cimma Nasarar Gudanar Da Gasar Mutum-Mutumin Inji Ta Kasa Da Kasa
  • Gaza : Spain ta bukaci kasashen duniya su kakabawa Isra’ila takunkumi
  • Falasdinawa 30 sun yi shahada a Wani harin Isra’ila kan wata makaranta
  • Rikici Ya Ɓarke Tsakanin ‘Yansanda Da Matasa A Rano, Mutum 1 Ya Mutu, An Harbi Wasu
  • Shugaban Shirin  HKI Da Amurkan  Na Raba Kayan Agaji A Gaza Ya Yi Murabus
  • ‘Yar Majalisar Dokokin Ireland Ta Yi Suka Kan Shugabannin Turai Tare Da Neman Afuwa Daga Falasdinawa
  • Tangarɗar Na’ura: JAMB Ta Sake Fitar Da Sakamakon Jarabawar UTME Ta 2025