Aminiya:
2025-09-18@02:19:02 GMT

’Yan sanda na neman ’yan bola-jari ruwa a jallo a Abuja 

Published: 10th, February 2025 GMT

’Yan sanda a Babban Birnin Tarayya Abuja sun buƙaci al’umma su kawo musu rahoton duk wanda aka ga yana sana’ar bola-jari a cikin gari.

Kwamishinan ’Yan Sanda na Abuja, Disu Olatunji, ne ya sanar da haka bayan taron Majalisar Tsaro ta Babban Birnin Tarayya wanda Minista Ezenwo Nyesom Wike ya jagoranta.

Idan ba a manta ba, a ranar 13 ga watan Janairu, 2025 ne Hukumar Babban Birnin Tarayya ta haramta ayyukan ’yan bola-jari a cikin faɗin birnin.

Umarnin ya taƙaita ayyukansu ga kan juji da ke ya yankunan da suke wajen birnin.

A lokacin zaman ne aka dakatar da ayyukan ’yan gwangwan na tsawon makonni biyu, saboda zargin alaƙarsu da ’yan bola-jari.

NAJERIYA A YAU: Shin Har Yanzu Akwai Masu Rufin Asiri A Najeriya? Ɗan sanda ya rataye kansa har lahira a Neja

An iya tuna cewa wannan lamari ya samo asali ne daga sace-sace kusan ɗauƙacin ƙarafunan murafen ramukan da ke kan titunan biran, waɗanda ake zargin ’yan bola-jari ne ke yi.

A yayin bincike da samame da aka kai a kasuwannin a sassan Abuja, jami’an tsaro sun gano ƙarafunan da wasu kayan gwamnati kamar fitilun kan titi da manyan wayoyin lantarki da sauransu a wurin wasu ’yan gwangwan.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Bola Jari Gwangwan yan bola jari

এছাড়াও পড়ুন:

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

 

Shugabannin biyu sun yi nazari kan muhimman fannonin hadin gwiwa tsakanin Nijeriya da Faransa, inda suka amince da zurfafa hadin gwiwa don samun ci gaban juna da kwanciyar hankali a duniya.

 

LEADERSHIP ta ruwaito cewa ba a bayar da wani dalili na sauya wannan hutun ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
  • Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
  • Likitoci Sun Tsunduma Yajin Aiki Na Dindindin A Abuja
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa