Xi: Kasar Sin A Shirye Take Ta Yi Aiki Da IOC Don Inganta Wasannin Olympic Na Duniya .

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Na Da Kwamitoci 30 Da Ke Sa Ido Kan Ma’aikatun Gwamnati

Majalisar Dokokin Jihar Jigawa ta ce akwai kwamitoci guda 30 da aka daurawa nauyin bibiyar yadda ma’aikatu da hukumomin gwamnatin Jihar ke sarrafa kudade domin gudanar da harkokin yau da kullum, gami da ayyukan raya kasa.

 

Shugaban Kwamatin kananan hukumomi na majalisar dokokin jihar, Alhaji Aminu Zakari, ya bayyana hakan lokacin wata ziyarar aiki a karamar hukumar Babura.

Yayi bayanin cewar, an dorawa Kwamatinsa alhakin duba kananan hukumomi domin tabbatar da shugabanci nagari a yankunan karkara.

 

A cewarsa, kwamatin yana duba kundin bayanan sha’anin mulki da na harkokin kudi da suka hada da jadawalin kudaden da karamar hukuma ke samu daga kason arzikin kasa, da littafin hulda da banki,da takardun biyan kudade na voucher da kundin bayanan tarukan kwamitocin karamar hukuma domin tabbatar da ritita kudaden gwamnati.

 

Alhaji Aminu Zakari ya kuma lura cewar, ziyarar tana bada damar ganawa tsakanin ‘yan kwamatin da masu ruwa da tsaki na kananan hukumomi domin tattaunawa da su, da nufin samar da kyakkyawan yanayin aiki tare tsakanin bangarori daban daban.

 

Karamin Kwamatin da wakilin mazabar Guri Alhaji Usman Abdullahi Tura Musari ya jagoranta, ya duba aikin noman shinkafa a fadamar Garu da ta Dangoriba da karamar hukumar Babura ta bullo da shi akan Kudi Naira Milyan 49 da dubu 500, inda aka samar da rijiyoyin ban ruwa dari-dari a kowacce fadama.

 

Alhaji Usman Musari ya kuma yabawa karamar hukumar Babura bisa kyakkyawar aniyarta, ta mara baya ga kokarin gwamnatin Malam Umar Namadi wajen bunkasa tattalin arzikin matasa ta fuskar hadahadar aikin noma.

 

A jawabin sa, shugaban karamar hukumar Babura Malam Hamisu Muhammad Garu, ya bayyana ziyarar a matsayin wani sanannen aiki da Majalisa ke yi duk shekara,  inda ya yi kira ga ma’aikata da ‘yan majalisar zartaswar karamar hukumar da su bada cikakken hadin kai domin samun nasarar ziyarar.

 

Sauran ‘yan kwamatin sun hada da mataimakin shugaban kwamatin kuma wakilin mazabar Kaugama Alhaji Sani Sale Zaburan da wakilin mazabar Kanya Babba Alhaji Ibrahim Hashim Kanya da mataimakan sakatare da Oditoci biyu.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki
  • Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United
  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Najeriya: Likitoci a Lagas Sun Shiga Yajin Aiki
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Na Da Kwamitoci 30 Da Ke Sa Ido Kan Ma’aikatun Gwamnati
  • ’Yan sa-kai aƙalla 100 da jami’an tsaro 30 sun mutu a bakin aiki a Katsina —Gwamnati
  • Pezeshkiya: Iran A Shirye Take Don Mu’amala Amma Bazata Bar Hakkinta Ba
  • Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Bukaci A Kara Inganta Aikin Titin Gabasawa
  • Araqchi: Tattaunawar Nukiliya Wani Zabi Ne Mai Muhaimmanci Wanda Ya Karfafa Matsayin Iran A Duniya