Kwara ta kammala horar da kwararrun ma’aikatan gona 1,000
Published: 7th, February 2025 GMT
Akalla manoma da ma’aikatan gona 1,000 ne gwamnatin jihar Kwara ta horas da su akan aikin gona da sarrafa ragowar amfanin gona don inganta amfanin gonakin da makiyaya ke amfani da su.
Da yake jawabi a karshen horon, a Ilorin, wanda Synergy Impact Limited ya shirya, tare da tallafin gwamnatin tarayya, bankin duniya da kuma shirin gwamnatin jihar Kwara akan kiyo da noma (L-PRES) kakakin majalisar dokokin jihar Kwara, Yakubu Danladi ya bayyana cewa shirin yana da karfin inganta ayyukan noma a jihar.
Kakakin majalisar wanda ya samu wakilcin shugaban kwamitin noma na majalisar, Issa Gideon, ya bayyana cewa shirin ya kara wa dimbin matasa kwarin gwiwa da jami’an noma da manoma wajen samar da kananan manaoma da sarrafa abincin dabbobi.
Ya godewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da gwamnatin jihar bisa bullo da shirin na L-PRES cewa aikin ya kara habaka noma a jihar.
Danladi, ya ce mahalarta taron, wadanda suka fito daga dukkan kananan hukumomin jihar 16, za su inganta harkar noma da kiwo a jihar da ma kasa baki daya.
Ya kuma bukaci mahalarta taron da su yi amfani da ilimin da aka samu a lokacin shirin, inda ya ce mutane na bukatar amfanin gona da kiwo a matsayin tushen arziki.
Dan majalisar ya ce samar da kananan dabbobin da matasa ke yi zai iya zama tushen gina tattalin arzikin kasar.
Ya kuma shawarci mahalarta taron da su kirkiro kayan aikin noma da injuna da aka samar musu a lokacin shirin horaswa a yankunansu daban-daban.
A nasa bangaren, shirin na jihar, Soji Oyawoye, ya bayyana fatansa cewa ilimi, kwarewa da kwarin gwiwa da mahalarta taron suka samu zai taimaka musu wajen aiwatar da ayyukan noma a yankunansu.
Ya kuma bukaci wadanda aka horas da su ma su horasda wasu akan wannan fasahar da suka samu ga manoma abokan aiki.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara mahalarta taron
এছাড়াও পড়ুন:
An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka
Bisa rahoton bunkasar hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da nahiyar Afirka na shekarar 2025, wanda aka gabatar a jiya Juma’a 13 ga wata, an ce a halin yanzu, an samu babban sauyi a tsarin ciniki tsakanin Sin da Afirka, an kuma kyautata tsarin zuwa mai shafar fannoni da dama, mai inganci, mai kunshe da fasahohin zamani, kana a nan gaba za a samu karin damar hadin gwiwarsu a fannonin masana’antu, da aikin noma, da sadarwa, da tattalin arziki ta yanar gizo, da ayyukan more rayuwa, da makamashi mai tsafta, da hada-hadar kudi da sauransu.
A matsayin daya daga cikin manyan nasarorin da aka cimma a gun bikin baje koli na tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Afirka karo na 4, an gabatar da rahoton ne a taron gabatar da shirye-shiryen ayyukan hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Afirka, wanda aka gudanar a wannan rana.
Rahoton ya yi bayanin cewa, a shekarun baya-baya nan, an fadada cinikayyar Sin da Afirka, yawan kudin cinikayyar kaya tsakaninsu a shekarar 2023 ya zarce dalar Amurka biliyan 280, kuma yawan kudin cinikin hidimomi a tsakaninsu a shekarar 2021 ya kai sama da dalar Amurka biliyan 41 da miliyan 866, kana an kyautata tsarin cinikinsu.
A daya bangaren kuma, yawan jarin da Sin ta zubawa Afirka ya karu, wanda yawancinsu suka shafi sha’anin gine-gine. Haka zalika, an samu nasarori a fannin gina ayyukan more rayuwa, da gudanar da ayyuka a fannonin sufuri, da wutar lantarki, da sadarwa, da madatsun ruwa da sauransu, da kuma yin hadin gwiwarsu a fannonin ba da ilmi, da aikin noma, da kiwon lafiya, da samun ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba da sauransu. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp