Kwara ta kammala horar da kwararrun ma’aikatan gona 1,000
Published: 7th, February 2025 GMT
Akalla manoma da ma’aikatan gona 1,000 ne gwamnatin jihar Kwara ta horas da su akan aikin gona da sarrafa ragowar amfanin gona don inganta amfanin gonakin da makiyaya ke amfani da su.
Da yake jawabi a karshen horon, a Ilorin, wanda Synergy Impact Limited ya shirya, tare da tallafin gwamnatin tarayya, bankin duniya da kuma shirin gwamnatin jihar Kwara akan kiyo da noma (L-PRES) kakakin majalisar dokokin jihar Kwara, Yakubu Danladi ya bayyana cewa shirin yana da karfin inganta ayyukan noma a jihar.
Kakakin majalisar wanda ya samu wakilcin shugaban kwamitin noma na majalisar, Issa Gideon, ya bayyana cewa shirin ya kara wa dimbin matasa kwarin gwiwa da jami’an noma da manoma wajen samar da kananan manaoma da sarrafa abincin dabbobi.
Ya godewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da gwamnatin jihar bisa bullo da shirin na L-PRES cewa aikin ya kara habaka noma a jihar.
Danladi, ya ce mahalarta taron, wadanda suka fito daga dukkan kananan hukumomin jihar 16, za su inganta harkar noma da kiwo a jihar da ma kasa baki daya.
Ya kuma bukaci mahalarta taron da su yi amfani da ilimin da aka samu a lokacin shirin, inda ya ce mutane na bukatar amfanin gona da kiwo a matsayin tushen arziki.
Dan majalisar ya ce samar da kananan dabbobin da matasa ke yi zai iya zama tushen gina tattalin arzikin kasar.
Ya kuma shawarci mahalarta taron da su kirkiro kayan aikin noma da injuna da aka samar musu a lokacin shirin horaswa a yankunansu daban-daban.
A nasa bangaren, shirin na jihar, Soji Oyawoye, ya bayyana fatansa cewa ilimi, kwarewa da kwarin gwiwa da mahalarta taron suka samu zai taimaka musu wajen aiwatar da ayyukan noma a yankunansu.
Ya kuma bukaci wadanda aka horas da su ma su horasda wasu akan wannan fasahar da suka samu ga manoma abokan aiki.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara mahalarta taron
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Gombe ta saurari ra’ayoyin jama’a kan kasafin kuɗin 2026
Gwamnatin Jihar Gombe ta ƙaddamar da taron sauraron ra’ayoyi jama’a kan shirye-shiryen tsara kasafin kuɗin shekarar 2026 a wani yunƙuri na jaddada ƙudirinta na gudanar da mulki cikin gaskiya da haɗin kai.
Da yake jawabi a wajen taron, Mataimakin Gwamnan Jihar, Dakta Manassah Daniel Jatau, ya bayyana cewa wannan mataki na nuna jajircewar Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya wajen tabbatar da cewa ra’ayoyin jama’a na taka muhimmiyar rawa a tsara kasafin kuɗi da aiwatar da shi.
Za a rataye wanda ya kashe ɗan uwansa a Ekiti Gobara ta tashi a babban kanti a AbujaYa ce tattaunawar ta bai wa gwamnati damar haɗa kai da sarakunan gargajiya, mata, matasa, ƙungiyoyin farar hula da sauran masu ruwa da tsaki, domin bayar da shawarwari kan muhimman fannoni kamar ilimi, lafiya, noma da gine-gine, da za su amfanar da al’umma baki ɗaya.
Dakta Jatau ya ƙara da cewa gwamnatin jihar ta samu ci gaba wajen alkinta kuɗaɗe cikin tsari da gaskiya, wanda hakan ya sa Gombe ke samun matsayi mai kyau a ɓangaren ingantaccen gudanar da kuɗi da sauƙin kasuwanci a Najeriya.
“Kasafin kuɗin 2026 zai mai da hankali ne kan ci gaba da ayyukan da ake yi, tare da ƙara zuba jari a muhimman fannoni, da tabbatar da daidaito da manufofin ci gaban ƙasa da na duniya,” in ji shi.
A nasa ɓangaren, Kwamishinan Kasafi da Tsare-Tsaren Tattalin Arziki, Alhaji Salihu Baba Alkali, ya bayyana taron a matsayin wata hanya ta buɗe ƙofa tsakanin gwamnati da jama’a domin samun fahimta da amincewa.
Ya buƙaci mahalarta taron da su bayar da shawarwari masu amfani da za su taimaka wajen samar da kasafin kuɗin da zai kasance mai ɗorewa kuma mai amfani ga kowa da kowa.
Kwamishinan ya kuma gode wa mahalartan bisa yadda suka bayar da gudunmawa, yana mai tabbatar da cewa za a yi la’akari da shawarwarinsu a cikin tsarin ƙarshe na kasafin kuɗin jihar.