Kazalika, a Arewacin Nijeriya, Robar Tumatir mai nauyin kilo 25  yanzu, ana sanar da ita kan Naira 6,500.

Shugabar kungiyar masu noman Tumatair da sarrafa shi ta kasa, Rabiu Zuntu ta sanar da cewa, an samu girbin Tumatir mai yawan gaske, duba da cewa; yanzu ana cikin watan Fabrairu, lokacin da ake samun yawaitarsa.

A cewar tata, tarin yawan nasa ne ya sa aka samu faduwar farashinsa a kasuwanni, wannan dalili ne ma ya sanya, don gudun kada manoman su yi asara; suke sayar da shi kan farashi mai sauki.

“Daga watannin Janairu, Fabrairu zuwa Maris; ana samun kwantan Tumatir, yanzu kuma muna da injinoni masu kyau na sarrafa Tumatirin, wanda hakan zai sa a samu raguwar farashin”, in ji Zuntu.

Har ila yau, Zuntu ta yi kira ga ‘yan Nijeriya da su yi amfani da wannan dama, domin sayen Tumatirn da yawa, kafin daga nan zuwa watan Afrilu.

“Akasari mukan bai wa masu amfani da kayan amfanin gona shawarar cewa, su sayi Tumatirin da dama a irin wannan lokaci, don adana shi”, a cewar ta Zuntu.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista

Ya ce Jihar Kurus Ribas ita ce ta farko a yankin kudu da ta shiga a dama da ita a harkar noman alkama, lamarin da ke nuni da gayar nasara wajen samar da abinci a kowani sassa na kasar nan.

Kyari ya kara da cewa shirin rabar da takin zamani ya taimaka wajen bunkasa samar da shinkafa zuwa tan 58,000, lamarin da ya bai wa gwamnatin tarayya sanya tallafi a bangaren rabar da shinkafa ga jihohin da ambaliyar ruwa ta shafa.

Ministan ya ce akwai bukatar kare masu amfani da kuma kayan da ake nomawa, “kaso 80 cikin 100 na abincinmu manoman cikin gida ne suka samar da su.”

A daidai gabar da ake hasashen adadin ‘yan Nijeriya zai kai miliyan 400 a nan da shekarar 2050, Kyari ya ce gwamnati ta dukufa wajen kyautata harkar noma da kuma samar wa matasa ayyukan yi a matsayin mataki mai dogon zango na samar da wadatar abincin.

Ya ce gwamnati na kuma kokarin gyara kadarorin da kasar ke da su kamar su taraktoci, da sauran muhimman kayan aiki domin kara bunkasa samar da abinci.

Ya kuma ce Nijeriya ta yi hadin gwiwa da kasar Belarus don samar da ayyukan hadaka da nufin kara yawan kayan da ake fitarwa.

Ministan ya yi gargadin cewa a guji amfani da injinan noma da gwamnati ta samar ba ta hanyoyin da suka dace ba, inda ya bukaci manoma da su yi amfani da irin wadannan kayan aikin yadda ya kamata.

Ministan ya ce warare uku na ajiyar kaya wato silo ne kawai suke aiki a halin yanzu, inda ya sha alwashin cewa za a maida hankali wajen gyara sauran.

Kyari ya ce “Ma’aikatar noma da dawata kasa da abinci za ta hada kai da masu ruwa da tsaki don tabbatar da an yi amfani da wadannan muhimman wuraren ajiyar kaya.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Iran, ta yi wa Isra’ila ruwan makamai masu linzami
  • Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
  • Gobara Ta Ƙone Wani Gidan Mai A Legas