Radio Nigeria Kaduna Sun Je Ta’aziyar Albabello
Published: 6th, February 2025 GMT
Mahukunta gidan Radiyon tarayya na kaduna sun kai wa iyalan Alhaji Bala Albabello ta”aziya wanda Allah ya yi wa rasuwa ranar litini 3 ga watan fabrairu na shekarar 2025.
Shugaban gidan Radion, Malam Buhari Awwalu ne ya jagoranci tawagar zuwa gidan marigayin dake Tudun Jukun a zaria.
Malam Buhari Awwalu ya jajantawa iyalan marigayin,inda ya yi addu’ar Allah ya bai iyalan hakurin rashin sa,kuma ya sa a rinka tunawa da kyawawan dabi’un sa na taimakawa marasa karfi da kuma Dora al’umma akan turbar kasuwanci.
Ya kuma roki Allah da ya sanya shi a aljannar firdausi.
Da ya ke jawabi a masadin iyalan,Alhaji Hassan Abdulwahab ya yi bayanin cewa marigayi Albabello ya sadaukar da rayuwar sa ce wajen hidimtawa al’umma.
Cikin mahukunta gidan Radion da suka rufa wa shugaban bayan sun hada mataimakin darakta mai kula da sashin mulki,Malam umar Alkali da mataimakin darakta mai kula da sashin shirye-shirye,Malam Idris Yahaya da mataimakin darakta mai kula da sashin talace-talace, Malam Musa Yahaya da mataimakin darakta mai kula da sashin cinikayya,Malam Abubakar Lawal Dutsen ma,da mataimakin darakta mai kula da wasanni da watsa shirye-shirye daga nesa,Malam Lawal Ali Garba da mai rikon shugaban sashin sabuwar hanyar yana labarai na zamani, Malam Umar usman Tsiga da shugaban sashin kula da na’urorin kwsmfuta,Malam Nasiru Umar chawai da mai binciken kudi,Malam Yusha’u Umar.
HALIRU HAMZA
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Ta aziya Zaria da mataimakin darakta mai kula da sashin
এছাড়াও পড়ুন:
An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
Ƙungiyar Malaman Makarantu ta Najeriya (NUT) reshen Jihar Gombe, ta ziyarci shugaban ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomi na jihar, Barista Sani Ahmad Haruna, a ofishinsa da ke Gombe.
Shugaban ƙungiyar, wanda shi ne shugaban Ƙaramar Hukumar Gombe, ya bayyana cewa gwamnati da shugabannin ƙananan hukumomi za su ci gaba da yin duk mai yiwuwa wajen inganta walwalar malamai.
Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyiYa ce: “Ba za mu taɓa barin malamai su shiga cikin matsanancin hali ba. Za mu duba matsalolinsu domin tabbatar da walwalarsu da ci gaban ilimi a jihar.”
Sani, ya kuma yaba da yadda NUT ke tattaunawa cikin lumana da kawo shawarwari maimakon ɗaukar matakan da za su iya kawo tsaiko ga harkar ilimi.
A nasa jawabin, shugaban NUT na jihar ya ce sun kai ziyarar ne domin tattauna matsalolin da malamai ke fuskanta, musamman na makarantun firamare da ƙananun sakandare da ke ƙarƙashin kulawar ƙananan hukumomi.
Ya ƙara da cewa manufar NUT ita ce samar da fahimtar juna da haɗin kai tsakaninsu da shugabannin ƙananan hukumomi domin gano hanyoyin magance matsaloli cikin lumana.