Radio Nigeria Kaduna Sun Je Ta’aziyar Albabello
Published: 6th, February 2025 GMT
Mahukunta gidan Radiyon tarayya na kaduna sun kai wa iyalan Alhaji Bala Albabello ta”aziya wanda Allah ya yi wa rasuwa ranar litini 3 ga watan fabrairu na shekarar 2025.
Shugaban gidan Radion, Malam Buhari Awwalu ne ya jagoranci tawagar zuwa gidan marigayin dake Tudun Jukun a zaria.
Malam Buhari Awwalu ya jajantawa iyalan marigayin,inda ya yi addu’ar Allah ya bai iyalan hakurin rashin sa,kuma ya sa a rinka tunawa da kyawawan dabi’un sa na taimakawa marasa karfi da kuma Dora al’umma akan turbar kasuwanci.
Ya kuma roki Allah da ya sanya shi a aljannar firdausi.
Da ya ke jawabi a masadin iyalan,Alhaji Hassan Abdulwahab ya yi bayanin cewa marigayi Albabello ya sadaukar da rayuwar sa ce wajen hidimtawa al’umma.
Cikin mahukunta gidan Radion da suka rufa wa shugaban bayan sun hada mataimakin darakta mai kula da sashin mulki,Malam umar Alkali da mataimakin darakta mai kula da sashin shirye-shirye,Malam Idris Yahaya da mataimakin darakta mai kula da sashin talace-talace, Malam Musa Yahaya da mataimakin darakta mai kula da sashin cinikayya,Malam Abubakar Lawal Dutsen ma,da mataimakin darakta mai kula da wasanni da watsa shirye-shirye daga nesa,Malam Lawal Ali Garba da mai rikon shugaban sashin sabuwar hanyar yana labarai na zamani, Malam Umar usman Tsiga da shugaban sashin kula da na’urorin kwsmfuta,Malam Nasiru Umar chawai da mai binciken kudi,Malam Yusha’u Umar.
HALIRU HAMZA
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Ta aziya Zaria da mataimakin darakta mai kula da sashin
এছাড়াও পড়ুন:
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
A nata bangare kuwa, Amurka ta bayyana aniyarta ta aiki tare da bangaren Sin, wajen ci gaba da warware sabani a fannonin tattalin arziki da cinikayya ta hanyar tsarin gudanar da shawarwari, da ingiza damar samar da karin nasarori daga tattaunawar, da kara samar da daidaito a alakar tattalin arziki da cinikayya tsakaninta da Sin.
Wakilin cinikayya na kasa da kasa na Sin karkashin ma’aikatar cinikayya, kuma mataimakin ministan cinikayyar kasar Li Chenggang, ya bayyana a yayin da yake yiwa manema labarai karin haske game da zaman tattaunawar sassan biyu. Ya ce sassan biyu suna sane da muhimmancin wanzar da daidaito, da kyautata alakar tattalin arziki mai nagarta tsakanin Sin da Amurka, sun kuma yi kyakkyawar musaya game da muhimman batutuwan cinikayya da na raya tattalin arziki dake jan hakulansu. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp