Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-05-01@04:36:17 GMT

Radio Nigeria Kaduna Sun Je Ta’aziyar Albabello

Published: 6th, February 2025 GMT

Radio Nigeria Kaduna Sun Je Ta’aziyar Albabello

Mahukunta gidan Radiyon tarayya na kaduna sun kai wa iyalan Alhaji Bala Albabello ta”aziya wanda Allah ya yi wa rasuwa ranar litini 3 ga watan fabrairu na shekarar 2025.

Shugaban gidan Radion, Malam Buhari Awwalu ne ya jagoranci tawagar zuwa gidan marigayin dake Tudun Jukun a zaria.

Malam Buhari Awwalu ya jajantawa iyalan marigayin,inda ya yi addu’ar Allah ya bai iyalan hakurin rashin sa,kuma ya sa a rinka tunawa da kyawawan dabi’un sa na taimakawa marasa karfi da kuma Dora al’umma akan turbar kasuwanci.

Ya kuma roki Allah da ya sanya shi a aljannar firdausi.

Da ya ke jawabi a masadin iyalan,Alhaji Hassan Abdulwahab ya yi bayanin cewa marigayi Albabello ya sadaukar da rayuwar sa ce wajen hidimtawa al’umma.

Cikin mahukunta gidan Radion da suka rufa wa shugaban bayan sun hada mataimakin darakta mai kula da sashin mulki,Malam umar Alkali da mataimakin darakta mai kula da sashin shirye-shirye,Malam Idris Yahaya da mataimakin darakta mai kula da sashin talace-talace, Malam Musa Yahaya da mataimakin darakta mai kula da sashin cinikayya,Malam Abubakar Lawal Dutsen ma,da mataimakin darakta mai kula da wasanni da watsa shirye-shirye daga nesa,Malam Lawal Ali Garba da mai rikon shugaban sashin sabuwar hanyar yana labarai na zamani, Malam Umar usman Tsiga da shugaban sashin kula da na’urorin kwsmfuta,Malam Nasiru Umar chawai da mai binciken kudi,Malam Yusha’u Umar.
HALIRU HAMZA

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Ta aziya Zaria da mataimakin darakta mai kula da sashin

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna

A Kaduna, an kama wasu mutane uku da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, ciki har da wani da ya ce ya koma jihar ne domin kafa sabuwar ƙungiya bayan an kama abokan aikinsa a Kwara.

Haka kuma, an kama wasu biyu da ke ɗauke da bindigogi.

‘Yansanda sun gano makamai da dama, ciki har da bindigogi ƙirar AK-47 da AK-49, da kuma wasu makamai da aka ƙera a gida.

Wannan aiki na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na yaƙar garkuwa da mutane da safarar makamai a faɗin ƙasar.

Kakakin rundunar, Olumuyiwa Adejobi, ya ce ana ci gaba da bincike, kuma za a gurfanar da waɗanda ake zargi a kotu da zarar an kammala binciken.

Ya kuma yaba da goyon bayan da al’umma da jami’an tsaro suka bayar wajen nasarar kama su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya
  • Hajj 2025: Kaduna Ta Gaddamar Da Ayarin Likitoci Da Za Su Kula Da Alhazan Jihar
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  • An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas
  • Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Sa’o’ii 72
  • Jihar Kebbi Ta Kammala Shirye-shiryen Aikin Hajjin 2025
  • Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran
  • Aikin Hajji: Za A Fara Jigilar Alhazan Jihar Kwara A Ranar 12 Ga Watan Mayu
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen
  • Falasdinu: Mahmud Abbas Ya Nada Magaji Da Kuma Mataimakasa