DeepSeek: Kawar Da Shinge Ta Hanyar Kirkiro Sabbin Fasahohi
Published: 5th, February 2025 GMT
Bisa wannan batu za mu iya ganin cewa, a wannan zamanin da muke ciki na samun ci gaban fasahohi cikin matukar sauri, ya kamata a kara nuna ra’ayi na bude kofa, da karfafa hadin gwiwa da cudanya da juna, maimakon nuna ra’ayin ‘yan mazan jiya da kasar Amurka da wasu kasashe suke yi, inda suke neman yin amfani da takunkumi da babakere wajen kiyaye fifikonsu a bangaren kimiyya da fasaha, matakin da ya raunana su ta fuskar karfin kirkiro sabbin fasahohi, abin da ya zama “Don auki ake yin kunu, ya koma ya rasa auki” ke nan.
Sai dai ko da yake batun nan ya kasance gargadi ga kasar Amurka da wasu, zai karfafa gwiwar ‘yan Afirka. A ganin masaniyar fasahar AI ‘yar kasar Ghana Rashida Musa, yadda kamfanin DeepSeek na Sin ya kawar da shingen da aka dasa masa ta hanyar kirkiro sabbin fasahohi, zai zama abin koyi ga matasan kasashen Afirka, don su raya kansu bisa shawo kan matsalolin da suke fuskanta a rayuwarsu ta yau da kullum. (Bello Wang)
এছাড়াও পড়ুন:
Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
Wani bon kirar hannu da aka dasa akan hanyar dake hada Rann da Gamboru a jihar Borno ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 6.
Daga cikin wadanda su ka rasa rayukansu sanadiyyar tashin bom din sun hada mata da kananan yara kamar yadda majiyar ‘yan sanda ta sanar.
Kungiyar nan mai suna; gwamnatin musulunci a yammacin Afirka ce ta sanar da daukar alhakin kai hari na ranar Litinin din da ta gabata.
Bugu da kari sauran wadanda su ka rasa rayukan nasu manoma ne da suke cikin motar a-kori-kura da ta taka nakiya.
Baya ga wadanda su ka rasa rayukansu, wasu mutanen su 3 sun jikkata,kuma tuni an dauke su zuwa asibiti domin yi musu magani.
Wani dan sintiri da yake aiki da rundunar fararen hula masu taimakawa jami’an tsaro, Abba Madu, ya shaida wa manema labaru cewa; Da alamu an dasa bom din domin ya tashi da jami’an tsaro da suke yin sintiri akan wannan hanyar.
Kungiyoyin ‘yan ta’adda sun saba dasa irin wadannan nakiyoyin da bama-baman akan hanyar da jami’an tsaro suke bi.
Kungiyar nan da take kiran kanta; Gwamnatin Musulunci a yammacin Afirka wacce a takaice ake kira; “ISWAP” ce ta dauki nauyin kai harin.
Tun a 2009 ne yankin Arewa maso gabashin kasar ta Najeriya yake fama da matsalar kungiyoyi masu dauke da makamai da su ka hada Bokoharam, sannan kuma daga baya waje 2016, kungiyar gwamnatin musulunci a yammacin Afirka.