Aminiya:
2025-11-03@14:01:46 GMT

Ma’auratan da aurensu ya mutu sau 12 a shekara 43

Published: 4th, February 2025 GMT

Wasu ma’aurata ’yan kasar Australia da suka yi aure kuma suka sake rabuwa da juna har sau 12 a cikin shekaru 43 da suka gabata, a yanzu ana gudanar da bincike a kan zargin zamba tsakaninsu.

’Yan sanda a birnin Vienna na kasar Australia a halin yanzu suna gudanar da bincike a kan wani lamari mai ban mamaki, inda wasu ma’aurata da suka yi aure sannan suka rabu har sau 12 a tsawon shekaru 43, domin yin amfani da wata doka da ta ba su damar karbar makudan kudade.

Dalilin da Tinubu ya ƙi amincewa da ƙudirin kafa Jami’ar Ilimi a Adamawa Don namen mulki ’yan siyasa ke sukan Tinubu —Gwamnan Kaduna

Ana zargin tsofaffin ma’auratan da laifin kitsa kowace rabuwa ce a takarda don matar ta samu a biya ta kudin sallama Dala 28,300 kwatankwacin Naira miliyan 43 da dubu dari 440 da dari 783, da aka ba ta bayan mutuwar mijinta na farko ta 1981.

Sun yi amfani da wata dokar kasar Australia da ta ba wa matan da ba su da aure damar a biya su kudin sallama matukar ba ta yi aure ba.

A kowace shekara biyu da rabi, za ta karbi fansho sau 2.5 na zaman zawarci na shekara-shekara, don haka duk shekara uku ko fiye da haka ita da mijinta na biyu za su rabu don ta sami kudin, sa’an nan kuma su sake yin wani auren.

Dabarar yaudarar ma’auratan ta bayyana ne a watan Mayun 2022 lokacin da Cibiyar Inshorar Fansho ta ki sake biyan matar da mijinta ya rasu kudin fansho, duk da rabuwarta a karo na 12 da mijinta na biyu.

Wani bincike ya nuna cewa, ma’auratan sun sake rabuwa, sannan suka yi gaggawar sake daura wani auren duk bayan shekaru uku, a daidai lokacin da matar za ta karbi kudin sallamarta.

Wani bincike da Hukumar Binciken Laifuka ta Graz ta gudanar ya nuna cewa, masu rabuwar auren sun kasance tare a gida daya, suna dafa abinci tare, har ma da kwanciya a gado tare.

A cewar makwabtan nasu, wadanda akasarinsu ba su da masaniya kan al’adar aurensu, sun kasance ma’aurata abin koyi kuma ba su taba rabuwa ba.

Halin nasu ya ankarar da hukuma gano cewa, suna amfani da wannan dabara sama da shekara arba’in.

Hukuncin da Kotun Koli ta yanke a ranar 12 ga Maris, 2024 ya bayyana cewa, “auren da ake yawan saki, sannan a sake daura auren a tsakanin ma’auratan cin zarafin doka ne, idan ba a fasa auren ba, kuma aka yi saki ne kawai don a tabbatar da biyan diyyar kudin fansho ga gwauruwar.”

Ma’auratan na fuskantar zargin yin zamba, inda masu gabatar da kara suka yi zargin cewa sun yi almubazzaranci da kudin sallamar da ya kai Dalar Amurka 341,000 kwantankwaci Naira miliyan 516 da dubu dari 761 da dari 483 da 37 a cikin shekara 43 da suka gabata.

Sai dai, hukumomin Australia ba su amince da rabuwar aure na 12 da ma’auratan suka yi ba, don haka ma’auratan za su fuskanci tuhuma tare.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Australia Ma aurata

এছাড়াও পড়ুন:

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

“Haka kuma an kama wata mata mai shekaru 34 da ake zargi da hannu a lamarin, tare da wasu masu gidan marayu guda biyu da ke Abuja da Jihar Nasarawa, inda aka gano wasu yaran da ake kyautata zaton an yi safarar su. Wasu daga cikin gidajen marayun da aka gano ana amfani da su ne a matsayin cibiyoyin ajiye yara, inda ake jiran ‘kwace’ ko sayar da su da sunan daukar nauyin marayu.”

Ya ce, “An gano gidajen marayu guda hudu da ke Kaigini, Kubwa Edpressway Abuja; Masaka Area 1, Mararaba kusa da Abaca Road; da kuma Mararaba bayan Kasuwar Duniya suna da alaka da wannan kungiya, kuma ana ci gaba da bincike a kansu.”

Ya kara da cewa, daya daga cikin masu korafin ya bayyana cewa ya biya Naira miliyan 2.8 a matsayin kudin daukar yaro, sannan ya biya Naira 100,000 a matsayin kudin shawara ga daya daga cikin ‘yan kungiyar.

Sanarwar ta kara da cewa, “Wani mai korafi ya ce shi ma ya biya Naira miliyan 2.8 kudin daukar yaro da Naira 100,000 kudin shawara ga wani dan kungiyar.

“An canza sunayen yawancin yaran da aka ceto, lamarin da ya kara wahalar da bincike da gano asalinsu,” in ji sanarwar.

Darakta Janar ta NAPTIP, Binta Adamu Bello, ta bayyana damuwarta kan wannan lamari, inda ta ce safarar yara ta zama babbar matsala a kasa.

Ta hanyar Adekoye, DG din ta nuna damuwa game da yadda wasu gidajen marayu ke amfani da raunin jama’a wajen aiwatar da safarar yara.

Ta ce, “Abin takaici ne yadda wasu masu mugunta da ke da sunayen kwararru da matsayi a cikin al’umma, suke amfani da matsayin su wajen yaudarar mutanen da ke cikin mawuyacin hali, su yi safarar ‘ya’yansu, da dama daga cikinsu ma sun tsira ne daga halaka a lokacin rikice-rikicen al’umma ko na manoma da makiyaya, sannan a sayar da su ga iyaye masu neman haihuwa a matsayin daukar yaro ba tare da sahihin izinin iyayensu ba.

“Wannan abin ba za a yarda da shi ba, kuma wadanda aka kama kan wannan mugun aiki za su fuskanci hukuncin doka yadda ya kamata.

“’Ya’yanmu ba kayayyaki ba ne da za a ajiye su a gidajen marayu a sayar ga mai biyan mafi tsada. Wannan dole ya tsaya,” in ji ta.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa November 1, 2025 Manyan Labarai Jerin Gwarazan Taurarinmu November 1, 2025 Manyan Labarai Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sudan : Mutane 1,500 sun rasa matsugunansu sakamakon tashin hankali
  • Matar aure ta yanka wuyan mijinta, ta fasa masa ido da wuƙa a Neja
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA