Aminiya:
2025-06-16@02:18:32 GMT

Ma’auratan da aurensu ya mutu sau 12 a shekara 43

Published: 4th, February 2025 GMT

Wasu ma’aurata ’yan kasar Australia da suka yi aure kuma suka sake rabuwa da juna har sau 12 a cikin shekaru 43 da suka gabata, a yanzu ana gudanar da bincike a kan zargin zamba tsakaninsu.

’Yan sanda a birnin Vienna na kasar Australia a halin yanzu suna gudanar da bincike a kan wani lamari mai ban mamaki, inda wasu ma’aurata da suka yi aure sannan suka rabu har sau 12 a tsawon shekaru 43, domin yin amfani da wata doka da ta ba su damar karbar makudan kudade.

Dalilin da Tinubu ya ƙi amincewa da ƙudirin kafa Jami’ar Ilimi a Adamawa Don namen mulki ’yan siyasa ke sukan Tinubu —Gwamnan Kaduna

Ana zargin tsofaffin ma’auratan da laifin kitsa kowace rabuwa ce a takarda don matar ta samu a biya ta kudin sallama Dala 28,300 kwatankwacin Naira miliyan 43 da dubu dari 440 da dari 783, da aka ba ta bayan mutuwar mijinta na farko ta 1981.

Sun yi amfani da wata dokar kasar Australia da ta ba wa matan da ba su da aure damar a biya su kudin sallama matukar ba ta yi aure ba.

A kowace shekara biyu da rabi, za ta karbi fansho sau 2.5 na zaman zawarci na shekara-shekara, don haka duk shekara uku ko fiye da haka ita da mijinta na biyu za su rabu don ta sami kudin, sa’an nan kuma su sake yin wani auren.

Dabarar yaudarar ma’auratan ta bayyana ne a watan Mayun 2022 lokacin da Cibiyar Inshorar Fansho ta ki sake biyan matar da mijinta ya rasu kudin fansho, duk da rabuwarta a karo na 12 da mijinta na biyu.

Wani bincike ya nuna cewa, ma’auratan sun sake rabuwa, sannan suka yi gaggawar sake daura wani auren duk bayan shekaru uku, a daidai lokacin da matar za ta karbi kudin sallamarta.

Wani bincike da Hukumar Binciken Laifuka ta Graz ta gudanar ya nuna cewa, masu rabuwar auren sun kasance tare a gida daya, suna dafa abinci tare, har ma da kwanciya a gado tare.

A cewar makwabtan nasu, wadanda akasarinsu ba su da masaniya kan al’adar aurensu, sun kasance ma’aurata abin koyi kuma ba su taba rabuwa ba.

Halin nasu ya ankarar da hukuma gano cewa, suna amfani da wannan dabara sama da shekara arba’in.

Hukuncin da Kotun Koli ta yanke a ranar 12 ga Maris, 2024 ya bayyana cewa, “auren da ake yawan saki, sannan a sake daura auren a tsakanin ma’auratan cin zarafin doka ne, idan ba a fasa auren ba, kuma aka yi saki ne kawai don a tabbatar da biyan diyyar kudin fansho ga gwauruwar.”

Ma’auratan na fuskantar zargin yin zamba, inda masu gabatar da kara suka yi zargin cewa sun yi almubazzaranci da kudin sallamar da ya kai Dalar Amurka 341,000 kwantankwaci Naira miliyan 516 da dubu dari 761 da dari 483 da 37 a cikin shekara 43 da suka gabata.

Sai dai, hukumomin Australia ba su amince da rabuwar aure na 12 da ma’auratan suka yi ba, don haka ma’auratan za su fuskanci tuhuma tare.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Australia Ma aurata

এছাড়াও পড়ুন:

Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi

Tsohon Gwamnan Jihar Ekiti, Kayode Fayemi, ya ce har yanzu Najeriya ba ta kai matsayin cin ribar cikakkiyar dimokuraɗiyya ba, duk da cewa an dawo mulkin farar hula shekaru 26 da suka gabata.

Yayin wata tattaunawarsa da gidan talabijin na Channels, domin bikin Ranar Dimokuraɗiyya, Fayemi ya bayyana cewa duk da cewa ana gudanar da zaɓe a kai a kai a ƙasar, har yanzu an rasa muhimman abubuwan da suka kamata su kasance a tsarin dimokuraɗiyya na gaskiya.

Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna

“Bai kamata mu rikita gudanar da zaɓe da aiwatar da dimokuraɗiyya ba,” in ji shi.

“Abin da muka samu a 1999 shi ne ’yancin zaɓar shugabanni, amma hakan kawai ɓangare ne guda ɗaya.

“Abin da muke da shi mulkin farar hula ne, ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba.”

Ya ce an samu ci gaba a ƙarƙashin gwamnatoci daban-daban tun daga baya, amma har yanzu Najeriya na buƙatar ƙarfafa al’adar dimokuraɗiyya da sauye-sauyen da suka dace.

Fayemi ya kuma tuna da lokacin da ya kasance ɗaya daga cikin masu fafutukar dimokuraɗiyya a zamanin mulkin soja, musamman a lokacin marigayi Janar Sani Abacha.

Ya bayyana yadda suka gudanar da shirye-shirye a wani gidan rediyo a aka ɓoye, don ƙalubalantar gwamnatin soji.

“Ba wai rashin tsoro ba ne, mun san hatsarin da ke tattare da lamarin, amma mun yi imani da abin da muke yi,” in ji shi.

“Na taɓa ɗaukar na’urar watsa shirye-shiryen rediyon Kudirat a cikin jirgin Air France da ya sauka a Legas lokacin da fafutukar ta yi zafi. Wannan kaɗai na iya jefa ni cikin hatsari.”

Ya ce waɗanda suka mutu a lokacin ba don sakaci suka rasa rayukansu ba, sai don sun gaskata ƙudurinsu na ganin an samu ’yanci.

Fayemi ya yaba wa Shugaba Bola Tinubu bisa karrama wasu daga cikin waɗanda suka fafata wajen dawo da dimokuraɗiyya.

Sai dai ya nuna damuwa cewa wasu da dama da suka taka muhimmiyar rawa a bayan fage ba a karrama su ba.

“Mutane da dama sun sa rayuwarsu cikin hatsari. Su ma sun cancanci a yaba musu.

“Ba daidai ba ne a girmama waɗanda ake gani a manta da waɗanda suka bayar da gudunmawarsu a bayan fage.”

Maganganun Fayemi sun haifar da zazzafar muhawara kan yadda Najeriya ke da buƙatar ci gaba kafin a kira ta da ƙasar da ke da cikakkiyar dimokuraɗiyya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa
  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba
  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawa guda bayan kwanaki 8
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje