Kungiyar Hamas Ta Bayyana Cewa A Shirye Take Ta Fara Tattaunawa, Marhala Ta Biyu Na Tsagaita Wuta A Gaza
Published: 4th, February 2025 GMT
Kungiyar Hamas wacce take iko da yanin zirin gaza ta bada sanarwan cewa a shirye take, masu shiga tsakanin, wato kasar Masar ta fara tattaunawa marhala ta biyu na tattaunawar tsagaita wuta a Gaza. Tashar talabijin ta Almayadeen ta kasar Lebanon ta nakalto kamfanin dillancin laran AFP na kasar Faransa yana fadar haka.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Tankokin Isra’ila sun kashe mutum 51 a wurin karbar abinci a Gaza
Tankokin yaƙin Isra’ila sun i kashe kimanin mutun 51 a yankin Khan Younis da ke Zirin Gaza, a yayin da mutanen suke tsaka da karbar abincin tallafi.
Jami’ain lafiya sun sun ce mutum 51 sun mutu, wasu 200 sun samu raunuka — 20 daga cikinsu suna cikin halin rai-kwakwai-mutu-kwakwai — bayan harin.
Sun bayyana harin a matsayin daya daga cikin mafiya muni da sojojin Isra’ila suka kai a baya-bayan nan a yayain da Falasdinawa ke kokarin samun abinci domin su rayu.
Bidiyon lamarin da suka karade kafofin sada zumunta sun nuna wasu gomman gawarwaki da ake zargin tankokin yakin Isra’ila sun mutsuttsuke a kan titi a Khan Younis.
Shaidu sun bayyana cewa sai da sojojin Isra’ilan suka sa mutanen suka taro a wuri guda sa’annan tankokin suka bude musu wuta.
Tankokin sun bude wuta ne a daidai lokacin da suke kokarin karbar tallafin abinci daga wata babbar motar kungiyar agaji.
Rundunar sojin Isra’ila ta tabbatar da aukuwar harin na ranar Litinin, wanda ta ce tana gudanar da bincike a kai.