HOTUNA: Hatsarin tirela ya yi ajalin mutum 4, shanu 15 da awaki 20 a Neja
Published: 4th, February 2025 GMT
Mutum huɗu sun riga mu gidan gaskiya yayin da wasu 13 suka jikkata a sanadiyyar wani mummunan hatsari da ya auku a hanyar Lapai zuwa Agaie da ke Jihar Neja.
Aminiya ta ruwaito cewa hatsarin ya rutsa da tireloli uku waɗanda suka yi karo da juna ’yar tazarar mitoci ƙalilan zuwa garin Agaie.
Mai gari ya tsere bayan mazauna sun cinna wa gidansa wuta a Kano NCDC ta tsaurara matakan shige da fice a Nijeriya saboda fargabar EbolaWani mazaunin yankin, Baba Yakubu ya bayyana cewa ɗaya daga cikin tirelolin da lamarin ya shafa ta ɗauko lodin dabbobi da suka haɗa da shanu da awaki
Shi ma Darekta Janar na Hukumar Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, Abdullah Baba Arah, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya bayyana cewa an miƙa waɗanda hatsarin ya rutsa da su zuwa Babban Asibitin Agaie domin samun kulawa.
Ya alaƙanta faruwar lamarin da saɓa wa ka’idar tuƙi a yayin da ɗaya daga cikin tirelolin ta yi ƙoƙarin ƙetare wadda ke gabanta ba bisa ka’ida ba.
Ya ce hatsarin ya yi ajalin mutum huɗu — biyu da suka mutu nan take, sai kuma wasu biyun da suka ce ga garinku nan bayan an miƙa su asibiti.
Kazalika, ya ce shanu kimanin 15 da fiye da awaki 20 sun mutu a dalikin hatsarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: awaki Hatsari Jihar Neja
এছাড়াও পড়ুন:
Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
Shugaban Amurka Donald Trump ya umarci jami’an hukumar kula da shige-da-ficen-kasar da su dakatar da aikin samamen kama baƙin-haure ’yan ci-rani, a gonaki da otal-otal da ma gidajen sayar da abinci na fadin kasar.
Jaridar New York Times ta Amurka ta rawaito ma’aikatar tsaron cikin gida na tabbatar da samun umarnin, wanda aka mika shi ga hukumar kula da shige-da-fice da kuma ta yaki da fasa-kwauri, to sai dai kamfanin dillancin labarai na Reuters bai kai ga tabbatar da sahihancin umarnin ba.
’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a GombeTun a lokacin yakin neman zaben shugabancin Amurka zango na biyu ,Mista Trump ya alkawarta korar bakin-hauren da suka shiga kasar ba bisa ka’ida ba.
To sai dai wannan mataki ya fuskanci kakkausan suka sakamakon yadda ake kame mutanen da ba su taba aikata laifin komai ba, musamman wadanda ke aiki a gonaki da sauran wurare, lamarin da ya janyo barkewar zanga-zanga a wasu sassan kasar.
Rahotanni sun tabbatar da cewa kawo yanzu an shafe kwanaki ana tarzoma a birnin Los Angeles na Jihar California ta Amurka, inda masu zanga-zanga ke dauki-ba-dadi da dakarun tsaron kasa da Shugaba Trump ya tura tun farko domin kwantar da zanga-zangar da ta barke sakamakon kamen bakin haure.