Aminiya:
2025-08-01@06:41:24 GMT

Rikicin rusau ya yi ajalin mutum 4 a Kano

Published: 3rd, February 2025 GMT

Aƙalla wasu mutum huɗu sun riga mu gidan gaskiya sakamakon ƙazamin rikicin da ya hautsinen tsakanin mahukunta da mazauna unguwar Rimin Auzinawa da ke Karamar Hukumar Ungogo a Jihar Kano.

Bayanai sun ce an harbe mutanen huɗu ne yayin da suka fito tirjiya kan rusau ɗin gine-gine da jami’an hukumar tsara birane ta Jihar Kano KNUPDA suka aiwatar.

NHIS: Kotu ta tsare Farfesa Usman Yusuf a Gidan Yarin Kuje Gwamnatin Najeriya za ta sake ƙara kuɗin lantarki

Majiyoyi sun shaida wa Aminiya cewa galibin gidajen da rusau ɗin ya shafa tuni KNUPDA ta shafa musu alamar cewa aiki zai biyo ta kansu.

Ana dai zargin cewa gine-ginen aƙalla 40 da mahukuntan suka rushe an yi su ne a kan fulotan Jami’ar Bayero da ke Kano.

Sai dai wani mazaunin yankin da ya zanta da Aminiya, ya ce tun da jimawa Hukumar ta KNUPDA ta warware wannan matsala kuma ta jaddada musu cewa a halastaccen matsuguninsu suke domin bai shiga harabar jami’ar ba.

“Mun jima da warware wannan matsala da KNUPDA. Sun tabbatar mana cewa gine-ginenmu ba su shiga harabar jami’ar ta Bayero ba.

“Amma kwatsam sai ranar Lahadi da daddare jami’an KNUPDA suka zo suka yi mana rusau.

“A yayin da wasu daga cikin mazauna suka yi ƙoƙarin tirjiya ne suka harbi mutum huɗu da yanzu an yi musu jana’iza. Wannan abun takaici ne.

Aminiya ta yi ƙoƙarin jin ta bakin Manajan Darekta na KNUPDA amma lamarin ya ci tura.

Kazalika, wakilinmu da ya ziyarci ofishin KNUPDA ya tarar da shi fayau a yayin da duk manyan jami’an sun ƙauracewa ofishin domin fargabar kawo musu harin ramuwa kamar yadda wani ƙaramin ma’aikaci ya tabbatar.

“Ana cikin wani yanayi na fargaba a ofishin nan. Shi ya sa ko wurin ajiyar motoci ya zama fayau don duk manyan ma’aikatan babu wanda ya shigo.

“Yanzu haka ƙananan ma’aikata ne kawai suke zaman dabaro a ofishin ba tare da sanin madafar da za a kama ba.

Wani babban Darektan KNUPDA da Aminiya ta tuntuɓa, ya ce ba ma’aikatansu ne suka yi rusau a unguwar ba, inda ya ba da tabbacin cewa jami’ai ne daga Ma’aikatar Ƙasa da Tsara Birane ne suka aiwatar da aikin.

Haka kuma, wani jami’i daga ma’aikatar wanda ya buƙaci a sakaya sunansa, ya ce wuraren da aka yi rusau mallakin Jami’ar Bayero ne kuma nan gaba kaɗan za a fitar da sanarwa a hukumance.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jami ar Bayero Jihar Kano Rimin Auzinawa

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma

Hukumar Kula da Jami’o’i ta Kasa (NUC) ta amince da fara karɓar dalibai a sabbin darussa guda shida a fannin noma a Jami’ar Jihar Gombe (GSU) a shekarar karatun 2025/2026.

Za a gudanar da shirye-shiryen ne a sabuwar Tsangayar Noma da aka kafa a garin Malam Sidi da ke Karamar Hukumar Kwami.

A ranar Litinin bayan taron majalisar gudanarwar jihar, Kwamishinan Noma da Kiwo, Barnabas Malle, ya bayyana cewa an amince da fara aikin sabuwar tsangayar aikin nomar ce ranar 21 ga Watan Mayu, 2025.

Sabbin darussan da aka amince da su sun haɗa da digir a bangaren Noma, Digiri a bangaren Gandun Daji da Dabbobin Jeji, Digiri a Kimiyyar Noma da Digiri a Kimiyyar Kasa, sai Digiri a fannin Tattalin Arzikin Noma.

Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri

Barnabas Malle ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta ware filin gona mai girman hektar 365 a Garin Tafida da ke Karamar Hukumar Yamaltu Deba, domin bincike da aikin gwaji na ɗalibai.

Ya kara da cewa ana kokarin samun ƙarin fili a Garin Kurugu da ke Karamar Hukumar Kwami, don fadada ayyukan kwalejin a nan gaba.

Kwamishinan Ilimi Mai zurfi, Shettima Gadam, ya kuma tabbatar da cewa NUC ta ba da cikakken izini ga jami’ar don fara daukar daliban ne a wadannan darussa daga shekarar karatun 2025/2026.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za a fara yi wa ɗaliban jami’o’i gwajin ƙwaya — Gwamnatin Nijeriya
  • Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine
  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Ambaliya ta yi ajalin mutum 30 a China
  • Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma
  • ‘Yan Sanda A Kano Sun Kama Kasurgumin Dan Fashin Nan Barga Da Wasu Mutum 14
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata