HausaTv:
2025-07-30@15:39:41 GMT

 Ana Ci Gaba Da Yi Wa Mutane Kisan Gilla A Kasar Syria

Published: 2nd, February 2025 GMT

Rahotanni da suke fitowa daga kasar Syria sun ce, ana ci gaba da yi wa daidaikun mutane kisan gilla a sassan kasar mabanbanta.

A kusa da garin Hamah, an kashe mutane 7 a bayana nan,  bayan da wasu masu dauke da makamai su ka shiga cikin garin Tal-Zahab. Masu dauke da bindigar sun kutsa gidan fararen hula tare da bude wuta a kansu.

Haka nan kuma maharan sun yi sata a cikin gidajen da su ka shiga.

An gano gawawwakin mutane 7 a cikin wadannan gidajen bayan ficewar maharan.  An harbi mutanan ne dai a kai da hakan ya yi sanadiyyar rasuwarsu.

Kamfanin dillancin larabdun “Sputnik” ya nakalto cewa, masu dauke da makaman sun kuma kame mutane da dama daga cikin wanann garin, tare da tafiyar da su zuwa wani  wuri da ba a san ko ina ne.

Da akwai tsoron cewa za a kashe wadannan mutanen da aka kama.

Wanann dai ba shi ne karon farko ba da ake yi wa fararen hula kisan gilla saboda banbancin akidarsu.

A bayan nan an kashe Dr. Hassan Ibrahim wanda yana daya daga cikin muhimman masu nazari da bincike a fagen ilimin kimiyya na kasar Syria, an kuwa tsinci gawarsa ne a garin “Ma’ariba” dake bayan birnin Damascus a ranar Asabar din da ta gabata. An kuma ga alamun azabtarwa kafin a kashe shi a sassan jikin nashi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Harin Ta’addanci A Wani Coci Ya Lashe Rayukan Mutane Fiye Da 21 A Gabashin Kongo

Fiye da mutane 21 ne suka mutu a wani harin ta’addanci da aka kai kan wani coci a gabashin Kongo

Rahotonni sun tabbatar da cewa; Sama da mutane 21 ne aka kashe a wani hari da mayakan ‘yan tawayen kungiyar Allied Democratic Forces (ADF) suka kai kan wani cocin Katolika da ke gabashin Kongo, wanda ya hada da kona gidaje da shaguna a yankin.

A ranar Lahadin da ta gabata ne mayakan da suke da alaka da kungiyar Allied Democratic Forces (ADF) da ke samun goyon bayan kungiyar ‘yan ta’adda ta ISIS suka kaddamar da harin ta’addanci kan wata majami’ar Katolika a gabashin Kongo.

“Sama da mutane 21 ne aka kashe a ciki da wajen cocin,” Dieudonné Duranthabo, wani jami’in kungiyoyin farar hula a Komanda, ya shaidawa kamfanin dillacin labarai na Associated Press cewa: “Sun gano akalla gawarwakin mutane uku da suka kone, sannan an kona gidaje da dama.”

Harin ya faru ne da misalin karfe 1:00 na safiyar Lahadi a cikin wani  cocin Katolika da ke yankin Komanda a gabashin Kongo. An kuma kona gidaje da shaguna da dama.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
  • Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar
  • Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri
  • Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu
  •  Rasha Ta Kai Munanan Hare-hare Akan Birnin Kiev Na Ukiraniya
  • Harin Ta’addanci A Wani Coci Ya Lashe Rayukan Mutane Fiye Da 21 A Gabashin Kongo
  • An Yanke Hukuncin Kisa Kan Yan MKO A Nan Iran