Aminiya:
2025-07-31@12:38:11 GMT

Asibitin Malam Aminu Kano ya hana motoci masu baƙin gilas shiga harabarsa

Published: 2nd, February 2025 GMT

A wani mataki na tsaro da Asibitin Koyarwa na Malam Aminu da ke Kano ya fitar saboda magance barazanar tsaro da yake fuskanta, ya fara aiwatar da dokar hana motoci masu baƙin gilas wato tinted glass shiga harabar asibitin.

Mahukuntan asibitin sun bayyana cewa, motocin da ke ɗauke da marasa lafiya ko ma’aikata za su iya shiga, amma sai an bi ka’idojin tsaro na musamman.

Mahaifin ma’aikacin Aminiya ya rasu Majalisar Matasa ta Ƙasa ta goyi bayan taron Kur’ani

A wata sanarwa da Daraktan Gudanarwa na asibitin, Usman Rabiu Mudi ya fitar, ya ce, an kafa dokar hana motocin masu baƙin gilashi shiga ne saboda wasu munanan abubuwan da suka faru.

Ya bayyana irin munanan ababen kamar yunƙurin sace mutane ta amfani da irin waɗannan motocin da kuma aikata ayyukan laifi daban-daban da suka ƙunshi sata da aikata abubuwan da ba su dace ba a cikin harabar asibitin.

Sanarwar ta ƙara da cewa, ma’aikatan asibitin da ke amfani da mota za su yi rajistar motocinsu a ofishin tsaro don samun tambarin tantancewa da izinin shiga.

A cewar rahotanni, satar motoci da babura da sauran kayayyaki masu daraja ta yi yawa a cikin harabar asibitin.

Haka kuma, an gano cewa, wasu mutane na amfani da harabar asibitin wajen aikata ayyukan ashsha, wanda hakan ya sa mahukuntan suka ɗauki wannan mataki na hana motoci masu baƙin gilashin shiga, don kare rayukan ma’aikata da marasa lafiya da baki.

Wani ɗalibi mai suna Ahmad Bala, wanda ya zo asibitin da mota mai baƙin gilashi, an dakatar da shi daga wurin jami’an tsaron da ke bakin ƙofa.

Ya ce, wannan doka tana da amfani, amma ya buƙaci a cire dalibai daga dokar.

“An dakatar da ni saboda baƙin gilashi, amma ni ɗalibi ne kuma ina goyon bayan wannan mataki.

“Amma ina ganin ya kamata a cire ɗalibai daga wannan doka saboda wannan asibitin koyarwa ne, kuma ɗalibai da dama suna zaune a cikin harabar asibitin,” in ji Bala.

Shugaban tsaro na asibitin, Sani Ahmad Mahmud ya bayyana cewa, matakin hana shigar motoci masu baƙin gilashin yana cikin manufofin kare ma’aikata da marasa lafiya da baƙi da ke zuwa asibitin.

“Wannan mataki ya zama wajibi saboda ƙalubalen tsaro da muke fuskanta. Ina kira ga jama’a su bi wannan doka tare da girmama ta, domin matakin yana cikin muradinsu,” in ji Mahmud.

Wasu daga cikin jama’a sun yaba da matakin, suna ganin hakan zai rage yawaitar shigar miyagun mutane cikin asibitin, inda suke amfani da damar babban harabar wajen aikata laifuka da ayyukan da ba su dace ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: harabar asibitin

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya amince da naɗa Muhammad Fa’iz a matsayin Kwamanda Janar na farko na Hukumar Hisbah ta Jihar.

Sakataren Gwamnatin Jihar Jigawa, Malam Bala Ibrahim, ne ya tabbatar da naɗin ga manema labarai a Dutse.

Ya bayyana cewa hakan na daga cikin ƙoƙarin Gwamna Namadi na ƙarfafa ayyukan sabuwar hukumar Hisbah da inganta aikinta.

A cewar sa, naɗin ya haɗa da Dr. Husaini Yusuf Baban a matsayin Babban Mataimakin Kwamanda Janar, da Lawan Danbala a matsayin Mataimakin Kwamanda Janar da hedikwatar hukumar, da kuma Yunusa Idris Barau a matsayin Mataimakin Kwamanda Janar naYankin Dutse.

Sauran su ne Abdulkadir Zakar, Mataimakin Kwamanda Janar, Yankin Hadejia, da Suraja Adamu, Mataimakin Kwamanda Janar, Yankin Gumel, da Bello Musa Gada, Mataimakin Kwamanda Janar, Yankin Kazaure, sai  Barrister Mustapha Habu a matsayin Sakatari kuma Lauya mai ba da shawara.

Malam Bala Ibrahim ya jaddada cewa an zaɓi waɗannan mutane ne bisa cancanta, ƙwarewa da kuma nagartar halayensu, yana mai kira gare su da su yi kokarin sauke nauyin da aka dora musu.

Sakataren Gwamnatin Jihar  ya ce an riga an mika musu takardun naɗi kuma sun shirya tsaf don fara aiki nan take.

A nasa bangaren, Muhammad Fa’iz ya gode wa Gwamna bisa amincewar da ya nuna musu, tare da alƙawarin gudanar da aiki da ƙwazo da himma.

 

 

Usman Muhammad Zaria 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Kula da Da’ar Ma’aikata Za Ta Fara Daukar Bayanai Ta Yanar Gizo
  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
  • Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Babu Wata Karamar Hukumar Dake Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
  • Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu
  • Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci
  •  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta
  • Mutum miliyan 1.2 na fama da ciwon hanta a Kano