An Kammala Aikin Tsugunar Da Mutane A Gundumar Tingri Ta Sin Bayan Bala’in Girgizar Kasa
Published: 1st, February 2025 GMT
A jiya Jamu’a, wakilin CMG ya samu labari daga ofishi mai kula da aikin ceton mutane daga bala’in girgizar kasa da ya abku a gundumar Tingri karkashin birnin Shigatse na kasar Sin cewa, yanzu haka, an kafa gidajen wucin gadi 7733, da tantuna 9941, tare da tsugunar da mutane 47787 da bala’in girgizar kasa ya ritsa da su.
A ranar 7 ga watan Janairun da ya gabata ne dai, aka samu abkuwar girgizar kasa da karfinta ya kai maki 6.8 a gudumar Tingri ta birnin Shigatse dake jihar Xizang ta Sin. Kana a halin yanzu, ban da mutanen da aka tsugunar da su cikin gidaje na wucin gadi da tantuna, ganin yadda bala’in girgizar kasa ya lalata gidajensu sosai, akwai wasu mutane 10772 da gidajensu ba su lalace sosai ba, wadanda aka yi bincike kan gidajensu, sa’an nan aka tabbatar da cewa za su iya ci gaba da rayuwa cikin tsoffin gidajensu, kuma babu bukatar tsugunar da su cikin gidajen wucin gadi ko tantuna. (Bello Wang)
কীওয়ার্ড: in girgizar kasa tsugunar da
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi
Shugaba Xi ya kuma bayyana cewa, cikakken zama na 4 na kwamiti na 20 na JKS ya amince da shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15. Sin za ta yi amfani da wannan damar don ci gaba da gyare-gyaren tattalin arzikinta, da kuma fadada bude kasuwancinta mai zurfi ga ketare, ta haka za ta ci gaba da ba da sabbin damammaki ga yankin Asiya da Pasifik da sauran kasashen duniya ta hanyar zamanantar da al’ummarta. (Amina Xu)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA