A jiya Jamu’a, wakilin CMG ya samu labari daga ofishi mai kula da aikin ceton mutane daga bala’in girgizar kasa da ya abku a gundumar Tingri karkashin birnin Shigatse na kasar Sin cewa, yanzu haka, an kafa gidajen wucin gadi 7733, da tantuna 9941, tare da tsugunar da mutane 47787 da bala’in girgizar kasa ya ritsa da su.

Wadannan alkaluma sun nuna cewa, an riga an kammala aikin tsugunar da dukkan mutanen wurin bisa wani mataki na wucin gadi.

A ranar 7 ga watan Janairun da ya gabata ne dai, aka samu abkuwar girgizar kasa da karfinta ya kai maki 6.8 a gudumar Tingri ta birnin Shigatse dake jihar Xizang ta Sin. Kana a halin yanzu, ban da mutanen da aka tsugunar da su cikin gidaje na wucin gadi da tantuna, ganin yadda bala’in girgizar kasa ya lalata gidajensu sosai, akwai wasu mutane 10772 da gidajensu ba su lalace sosai ba, wadanda aka yi bincike kan gidajensu, sa’an nan aka tabbatar da cewa za su iya ci gaba da rayuwa cikin tsoffin gidajensu, kuma babu bukatar tsugunar da su cikin gidajen wucin gadi ko tantuna. (Bello Wang)

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: in girgizar kasa tsugunar da

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe gomman mutane a ƙauyukan Sakkwato

An sake shiga tashin hankali a Jihar Sakkwato bayan wani sabon mummunan hari da ’yan bindiga suka kai a wasu kauyuka, lamarin da ke ƙara tsananta matsalar tsaro a faɗin jihar.

Rahotanni sun nuna cewa duk shekara musamman a lokacin damina, ’yan bindiga sukan ƙara ƙaimi wajen kai hare-haren da ke tarwatsa jama’a a garuruwansu da hana manoma zuwa gona ko kuma ƙaƙaba musu harajin zuwa gonakin.

An ɗaure tsohon Firaminista Succes Masra shekaru 20 a Chadi Dan wasan Barcelona Inigo Martinez ya koma Al-Nassr

Aminiya ta ruwaito cewa, a bana ma, maharan sun ci gaba da addabar mazauna ƙananan hukumomi 20 daga cikin 23 na Jihar Sakkwato.

Majiyoyi sun tabbatar cewa a harin baya-bayan nan, ’yan ta’addan sun hallaka mutane da dama sannan sun yi garkuwa da wasu.

Shafin Bakatsine da ke bibiyar rahotannin da suka shafi sha’anin tsaro, a wannan Lahadin ya wallafa a manhajar X cewa, an kai hari a wani masallaci a garin Bushe da ke Karamar Hukumar Sabon Birni, inda aka sace aƙalla mutum 10 ciki har da limamin masallacin.

Rundunar ’yan sandan jihar ta tabbatar da faruwar lamarin, tana mai cewa ana ci gaba da ƙoƙarin ceto waɗanda aka sace.

Haka kuma, rahotanni sun ce maharan sun sake kai wani hari a lokacin sallar Isha a ƙauyen Marnona na Karamar Hukumar Wurno, a daren Asabar, inda suka kashe masallata da dama sannan suka yi awon gaba da wasu.

Sanata Ibrahim Lamido, mai wakiltar Sakkwato ta Gabas a Majalisar Dattawa, ya yi Allah wadai da hare-haren da suka auku a Bushe da Marnona, inda ya buƙaci hukumomi su ƙara ƙaimi wajen kare rayuka da dukiyar al’umma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dasuki: Kotu ta bai wa Gwamnatin Tarayya wa’adin kammala shari’ar kuɗin makamai
  • Gaza: Yunwa ta kashe Falastinawa 5 a cikin kasa da Sa’o’i 24 da suka gabata
  • Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista
  • Hukumar Alhazai ta Jihar Kaduna Ta Bukaci Maniyyatan Aikin Hajjin 2026 Su Fara Biyan Kudaden Ajiya
  • Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu
  • ’Yan bindiga sun kashe gomman mutane a ƙauyukan Sakkwato
  • UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 
  • Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinu a Isra’ila da Pakistan
  • Birtaniya: ‘Yan sanda sun kama akalla mutane 365 a zanga-zangar goyon bayan Falasdinu
  • Yansanda A Burtaniya Ta kama Mutane Fiye Da 200 Masu Goyon Bayan Falasdinawa