Aminiya:
2025-09-18@02:18:50 GMT

Masu yi wa ƙasa hidima za su karɓi N77,000 daga Fabrairu – Shugaban NYSC

Published: 1st, February 2025 GMT

Shugaban Hukumar yi wa ƙasa hidima ta Najeriya, NYSC Birgediya Janar Yusha’u Dogara Ahmed ya tabbatar wa mambobin shirin da suke aikin yi wa ƙasa hidima na shekara ɗaya cewa za su fara karɓar Naira 77,000 daga watan Fabrairu.

A daidai lokacin da aka sake duba mafi ƙarancin albashi da hauhawar farashin kayayyaki, gwamnatin tarayya ta sanar da ƙarin kuɗaɗen alawus ɗin daga N33,000 zuwa N77,000 duk wata, amma da dama sun nuna damuwarsu kan aiwatar da hakan.

Gwamna Buni ya zama Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Tafkin Chadi ’Yan bindiga sun kashe mutum 3 sun sace 24 a Zamfara

A shekarar bara wani jami’in shirin ya danganta jinkirin aiwatar da biyan kuɗin da rashin kuɗi.

Amma yayin da yake bayani ga mambobin rukunin 2024 Batch ‘C’ Stream II a Jihar Katsina, Ahmed ya tabbatar da cewa an shigar da ƙarin kuɗin a kasafin kuɗin 2025.

Ya ce za a fara aiwatar da shi da zarar an zartar da kasafin kuɗin.

“Tuni gwamnatin tarayya ta amince da ƙarin kuɗaɗen alawus ɗin ku. Ba sabon labari ba ne; abin da muka amince ne da hannunmu. Abin da muke jira shi ne kawai aiwatar da kasafin kuɗin.

“Wannan watan (Janairu) ya riga ya ƙare, amma da zarar an gama kasafin kuɗin, nan da wata mai zuwa (Fabrairu), za ku fara karɓar Naira 77,000 maimakon N33,000 da aka saba karɓa.” In ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Birgediya Janar Yusha u Dogara Ahmed

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

“Sauran motocin da ke cikin ayarin, ciki har da wacce ke ɗauke da shugaban majalisar, da ƙyar suka iya tsayawa wanda tsakaninsu mitoci kaɗan ne daga wurin da haɗarin ya afku,” in ji wani ganau.

 

Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa, an garzaya da jami’an ‘yansandan da suka samu raunuka zuwa babban asibitin Gumel a sume amma daga baya sun farfaɗo.

 

Da yake magana kan lamarin, mataimakin shugaban majalisar, Aqeel Akilu, ya yi godiya ga Ubangiji cewa, ba a rasa rayuka ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin