Masu yi wa ƙasa hidima za su karɓi N77,000 daga Fabrairu – Shugaban NYSC
Published: 1st, February 2025 GMT
Shugaban Hukumar yi wa ƙasa hidima ta Najeriya, NYSC Birgediya Janar Yusha’u Dogara Ahmed ya tabbatar wa mambobin shirin da suke aikin yi wa ƙasa hidima na shekara ɗaya cewa za su fara karɓar Naira 77,000 daga watan Fabrairu.
A daidai lokacin da aka sake duba mafi ƙarancin albashi da hauhawar farashin kayayyaki, gwamnatin tarayya ta sanar da ƙarin kuɗaɗen alawus ɗin daga N33,000 zuwa N77,000 duk wata, amma da dama sun nuna damuwarsu kan aiwatar da hakan.
A shekarar bara wani jami’in shirin ya danganta jinkirin aiwatar da biyan kuɗin da rashin kuɗi.
Amma yayin da yake bayani ga mambobin rukunin 2024 Batch ‘C’ Stream II a Jihar Katsina, Ahmed ya tabbatar da cewa an shigar da ƙarin kuɗin a kasafin kuɗin 2025.
Ya ce za a fara aiwatar da shi da zarar an zartar da kasafin kuɗin.
“Tuni gwamnatin tarayya ta amince da ƙarin kuɗaɗen alawus ɗin ku. Ba sabon labari ba ne; abin da muka amince ne da hannunmu. Abin da muke jira shi ne kawai aiwatar da kasafin kuɗin.
“Wannan watan (Janairu) ya riga ya ƙare, amma da zarar an gama kasafin kuɗin, nan da wata mai zuwa (Fabrairu), za ku fara karɓar Naira 77,000 maimakon N33,000 da aka saba karɓa.” In ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Birgediya Janar Yusha u Dogara Ahmed
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Ivory Coast Ouattara zai sake takara wa’adi na huɗu
Shugaban Ivory Coast, Alassane Ouattara wanda ke jagorantar ƙasar tun daga shekarar 2011, na fuskantar suka na neman mayar da shugabancin ƙasar mutu ka raba.
Wannan dai na zuwa ne bayan Ouattara mai shekaru 83 ya tabbatar da aniyar sake takara wa’adi na hudu a zaben da za a yi ranar 25 ga watan Oktoba.
Za mu halasta kafa ƙasar Falasɗinu muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba — Birtaniya Nijar da Rasha sun ƙulla yarjejeniyar makamashin nukiliyaA wani takaitaccen bayani da ya yi, Ouattara ya ce takararsa ta samo asali ne daga buƙatarsa ta kiyaye zaman lafiyar ƙasa a daidai lokacin da ta ke fuskantar kalubalen tsaro da na tattalin arziki.
Ya bayyana cewa, “Ni dan takara ne saboda kundin tsarin mulkin kasarmu ya ba ni damar sake tsayawa takara a wani wa’adi, kuma ina da lafiyar yin hakan,” inji Shugaba Ouattara.
Sanarwar da ya yi a kafafen sada zumunta, na zuwa ne bayan da jam’iyyarsa ta Rally of Houphouëtists for Democracy and Peace (RHDP) ta amince da takararsa a hukumance.
Jam’iyyun adawa sun soki matakin da cewa ya saba wa kundin tsarin mulkin kasar.
Tun dai gabanin sanar da matsayar sake takara, aka soma tafka muhawara kan soke sunayen ’yan takarar shugaban kasa daga bagaren ’yan adawa.
Tsohon shugaban ƙasar Laurent Gbagbo, da tsohon Firaminista Guillaume Soro, da kuma tsohon minista Tidjane Thiam duk an cire sunayensu daga rajistar masu zaɓe, lamarin da ya hana su tsayawa takara.
Bayanai sun ce hankali ya ƙara tashi a yau bayan da hukumomi suka haramta zanga-zangar lumana da aka shirya gudanarwa a ranar 7 ga watan Agusta, ranar bikin samun ’yancin kai na Cote d’Ivoire.
Ƙungiyoyin ’yan adawa ne suka shirya zanga-zangar da nufin neman a gudanar da bincike mai zaman kansa kan jerin sunayen masu kaɗa ƙuri’a tare da mayar da sunayen waɗanda aka hana tsayawa takara.