Ya tona kabarin mijin mahaifiyarsa ya yanke kansa a Adamawa
Published: 31st, January 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Jihar Adamawa ta kama wani mafarauci mai shekara 55 mai suna Yusuf Garba wanda aka fi sani da Gana kan zarginsa da tona kabari tare da yanke kan mijin mahaifiyarsa.
A cewar jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan, SP Suleiman Yahaya Nguroje, wanda ake zargin ya amsa laifinsa ne a lokacin da ake masa tambayoyi.
Garba wanda ɗan asalin garin Tappare Kona Uku ne a ƙaramar hukumar Jada ta jihar, ya bayyana cewa ɗan marigayin ne ya tuntuɓe shi inda ya buƙaci kan mijin mahaifiyarsa don yin tsafi bayan rasuwarsa.
Shekara guda bayan binne shi, ɗan ya dawo ya nemi kan mijin mahaifiyarsa don yin tsafin al’adun gargajiya.
Garba ya yi iƙirarin cewa ɗan mijin mahaifiyarsa ne ya matsa masa lamba, wanda ya yi imanin matsafi ne kuma zai iya cutar da shi ko kuma ‘ya’yansa idan ya ƙi bin umarninsa.
Ya ce, “Na ɗauki fartanya da misalin ƙarfe 4:00 na asubahi, na je maƙabarta, na tona kabari, na yanke kan sa.
Sai ya dawo gida ya ba wa yaron kan a cikin jakar leda.
Wanda ake zargin ya ci gaba da bayanin cewa bayan mako biyu, matar marigayin ta zo wurinsa inda ta shaida masa cewa ta yi munanan mafarki tun lokacin da aka ajiye kan a ɗakin kwanansu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Adamawa kabari mijin mahaifiyarsa
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Duk wani harin wuce gona da iri kan Iran zai fuskanci mayar da martani daidai da shi cikin gaggawa
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya tabbatar da cewa Iran na da kwarin gwiwa kan iya dakile duk wani yunkuri da wasu bangarorin ke yi na kawo cikas ga manufofinta na ketare.
Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araqchi ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa: Rudun gwamnatin yahudawan sahayoniyya, wadda take ganin za ta iya gindaya wa Iran abin da ya kamata ko kuma bai kamata ba, rudun tunani ne da ya yi nesa da hakikanin gaskiya, ta yadda bai cancanci mayar da martani ba.
Araqchi ya kara da cewa: “Duk da haka, jajircewar Netanyahu wani abin lura ne, a yayin da yake kokarin neman bayyana wa Shugaba Trump abin da zai iya ko kuma ba zai iya yi a diflomasiyyarsa da Iran ba!”
Ministan harkokin wajen ya yi nuni da cewa: “Abokanan Netanyahu a cikin tawagar Biden da ta gaza – wadanda suka kitsa makarkashiyar hana cimma yarjejeniya da Iran – suna kokarin nuna zaman tattaunawar da ake yi ba na kai tsaye ba da gwamnatin Trump a matsayin wani kuskure ne kuma tamkar hoton sauran yarjejeniyar nukiliya ce da aka gudanar.”