Ya tona kabarin mijin mahaifiyarsa ya yanke kansa a Adamawa
Published: 31st, January 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Jihar Adamawa ta kama wani mafarauci mai shekara 55 mai suna Yusuf Garba wanda aka fi sani da Gana kan zarginsa da tona kabari tare da yanke kan mijin mahaifiyarsa.
A cewar jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan, SP Suleiman Yahaya Nguroje, wanda ake zargin ya amsa laifinsa ne a lokacin da ake masa tambayoyi.
Garba wanda ɗan asalin garin Tappare Kona Uku ne a ƙaramar hukumar Jada ta jihar, ya bayyana cewa ɗan marigayin ne ya tuntuɓe shi inda ya buƙaci kan mijin mahaifiyarsa don yin tsafi bayan rasuwarsa.
Shekara guda bayan binne shi, ɗan ya dawo ya nemi kan mijin mahaifiyarsa don yin tsafin al’adun gargajiya.
Garba ya yi iƙirarin cewa ɗan mijin mahaifiyarsa ne ya matsa masa lamba, wanda ya yi imanin matsafi ne kuma zai iya cutar da shi ko kuma ‘ya’yansa idan ya ƙi bin umarninsa.
Ya ce, “Na ɗauki fartanya da misalin ƙarfe 4:00 na asubahi, na je maƙabarta, na tona kabari, na yanke kan sa.
Sai ya dawo gida ya ba wa yaron kan a cikin jakar leda.
Wanda ake zargin ya ci gaba da bayanin cewa bayan mako biyu, matar marigayin ta zo wurinsa inda ta shaida masa cewa ta yi munanan mafarki tun lokacin da aka ajiye kan a ɗakin kwanansu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Adamawa kabari mijin mahaifiyarsa
এছাড়াও পড়ুন:
Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
Shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar amfani da ƙarfin soji kan Najeriya matuƙar gwamnatin ƙasar ba ta dakatar da kisan da ’yan ta’adda masu iƙirarin jihadi ke yi wa Kiristoci ba.
A yammacin jiya Asabar ne Trump ya umarci Ma’aikatar Yaƙin Amurka ta Pentagon da ta soma tsara yadda za a kai hari Nijeriya bayan da ya yi zargin cewa ana yi wa Kiristoci kisan gilla a ƙasar.
Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, Trump ya ce Amurka a shirye ta ke ta aike da sojoji da manyan makamai cikin Najeriya don bai wa Kiristocin kariya.
Barazanar shugaban na Amurka na zuwa ne kwana guda bayan ya yi iƙirarin cewa an kashe Kiristoci aƙalla 3,100 a Nijeriya ba tare da ya bayyana takamaimai inda ya samu waɗannan alƙaluma ba.
“Muddin gwamnatin Nijeriya ta ci gaba da bari ana kashe Kiristoci, Amurka za ta dakatar da dukkan tallafin da take bai wa Nijeriya nan-take, kuma mai yiwuwa za ta shiga wannan ƙasƙantacciyar ƙasar, cike da ƙarfin gwiwa domin kawar da ’yan ta’adda masu kaifin kishin Musulunci waɗanda ke yin wannan ta’asa,” in ji Trump.