Tankar fetur ta yi bindiga a gidan mai Jigawa
Published: 31st, January 2025 GMT
Wata tankar mai cike da fetur ta yi bindiga a cikin wani gidan mai da ke garin Dutse, hedikwatar Jihar Jigawa.
A safiyar Juma’a ne kakakin ’yan sanda a Jihar Jigawa, SP Shiisu Adamu, ya sanar cewa lamarin ya faru ne a gidan mai na Shakkato da ke kan hanyar Kiyawa.
Hakan na zuwa ne yayin da aka samu karuwar fashewar tankoki dauke da man fetur a Najeriya, wanda mafi muninsu a baya-bayan nan ya yi ajalin sama da mutum 100 a Jihar Neja.
Ko a shekarar da ta gabata, irin haka ya faru a Jihar Jigawa, inda sama damutum 100 suka rasu.
Seaman Abbas da Hussaina: An dakatar da shirin Brekete Family Hausa An ɗaure zawarawa a gidan yari kan aikata zinaDa yake tabbatar cewa abin ya auku ne a ranar Alhamis, SP Shiisu Adamu ya bayyana cewa, amma ba a samu asarar rai ba.
Ya ce binciken farko ya nuna tankar man fetur din ta kama da wuta ne a yayin da motar take kokarin sauke man da ta dauko a gidan man.
“Kafin kiftawa da Bismillah wutar ta yi girma fiye da misali inda nan take aka kira hukumar kashe gobara, ta gaggauta zuwa tare da nasarar shawo kan lamarin.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Jigawa tankar mai
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yansan Jigawa Sun Tabbatarwa Mafarauta Da ‘Yan Bulala Samun Horo
Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta tabbatar wa kungiyar mafarauta/Yanbulala reshen jihar Jigawa na rundunar a shirye ta ke ta shirya wani horo na kara musu karfin gwiwa ga mambobinsu.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Dahiru Muhammad ya bayar da wannan tabbacin ne a yayin wani taro da aka yi da mafarauta/Yanbulala na yankin wanda Lamido Wada ya jagoranta a Dutse babban birnin jihar.
Ya bayyana cewa, Rundunar za ta hada gwiwa da wadanda abin ya shafa domin fuskanatar kalubalen zirga-zirga don daukar matakin da ya dace.
A cewarsa, rundunar ta ci gaba da shirye-shiryen ‘yan sanda da al’umma ke tafiyar da su ta hanyar samar da hadin gwiwa mai karfi da masu ruwa da tsaki da suka himmatu wajen samar da zaman lafiya da tsaro a fadin jihar.
Dahiru Muhammad ya bayyana jin dadinsa da irin dimbin karfin da suke da shi, da tsari, da tsarin jagoranci.
A yayin ziyarar, maziyartan sun yi alkawarin ci gaba da jajircewarsu wajen kiyaye dazuzzuka da kuma tabbatar da tsaro a fadin jihar.
Sannan sun gabatar da muhimman bukatu ga kwamishinan ‘yan sanda, wadanda suka hada da samar da hanyoyin sadarwa da ayyukansu ga babbar hukuma, jami’an tsaro, da sauran masu ruwa da tsaki ta hanyar CP a matsayin hanyar tuntubar juna.
Shirya horar da ƙwararrun mambobi don haɓaka ƙarfin aikinsu da tabbatar da suna aiki daidai da buƙatun doka.
Sauran buƙatun sun haɗa da samar da tallafin abin hawa, kamar babura, don sauƙaƙe ayyukan su.
Taron ya hada wakilai uku da suka hada da shugaba, Kwamanda, da Sakatare daga kowace karamar hukuma 27 dake fadin jihar.
Tawagar ta kuma samu rakiyar Salisu Garba Kubayo, babban mataimaki na musamman kan hukumar manoma da makiyaya ga Gwamna Umar Namadi.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, kungiyar ‘yan kabilar Igbo reshen jihar karkashin jagorancin Cif Christopher Agbo ta kai ziyarar ban girma ga kwamishinan ‘yan sanda.
Kungiyar ta bayyana kudirinta na tallafawa ‘yan sanda wajen wanzar da zaman lafiya, tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi, da kuma samar da yanayi mai kyau na kasuwanci da zamantakewa a fadin jihar.
KARSHE/USMAN MZ