Tankar fetur ta yi bindiga a gidan mai Jigawa
Published: 31st, January 2025 GMT
Wata tankar mai cike da fetur ta yi bindiga a cikin wani gidan mai da ke garin Dutse, hedikwatar Jihar Jigawa.
A safiyar Juma’a ne kakakin ’yan sanda a Jihar Jigawa, SP Shiisu Adamu, ya sanar cewa lamarin ya faru ne a gidan mai na Shakkato da ke kan hanyar Kiyawa.
Hakan na zuwa ne yayin da aka samu karuwar fashewar tankoki dauke da man fetur a Najeriya, wanda mafi muninsu a baya-bayan nan ya yi ajalin sama da mutum 100 a Jihar Neja.
Ko a shekarar da ta gabata, irin haka ya faru a Jihar Jigawa, inda sama damutum 100 suka rasu.
Seaman Abbas da Hussaina: An dakatar da shirin Brekete Family Hausa An ɗaure zawarawa a gidan yari kan aikata zinaDa yake tabbatar cewa abin ya auku ne a ranar Alhamis, SP Shiisu Adamu ya bayyana cewa, amma ba a samu asarar rai ba.
Ya ce binciken farko ya nuna tankar man fetur din ta kama da wuta ne a yayin da motar take kokarin sauke man da ta dauko a gidan man.
“Kafin kiftawa da Bismillah wutar ta yi girma fiye da misali inda nan take aka kira hukumar kashe gobara, ta gaggauta zuwa tare da nasarar shawo kan lamarin.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Jigawa tankar mai
এছাড়াও পড়ুন:
Jaridar The Guardian Mafi Yawan ‘Yan Gudun Hijiran Sudan Ne A Gidan Yarin Kasar Girka
Jaridar The Guardian ta Buga Labarin Cewa: Gidajen yarin Girka sun cika makil da ‘yan gudun hijirar Sudan
Jaridar The Guardian ta kasar Britaniya ta ruwaito cewa: Mahukuntan kasar Girka na tsare da daruruwan bakin haure ba bisa ka’ida ba a karkashin wata doka mai tsauri da ta fara aiki a shekara ta 2014 kuma dokar ta kunshi hukunta masu laifin daurin shekaru 25 a gidan yari.
Jaridar ta The Guardian ta ruwaito cewa: Masu fasakwaurin mutane da aka yanke wa hukunci sun zama rukuni na biyu mafi girma a gidajen yarin Girka, bayan masu safarar miyagun kwayoyi.
Jaridar ta bayyana cewa ‘yan Sudan su ne rukuni na hudu mafi girma na masu neman mafaka a kasar Girka, inda suka zarce ‘yan ciranin gargajiya na wasu kasashe kamar ‘yan Siriya da Falasdinawa.