Jadawalin Gasar AFCON 2025 da za a fafata a Morocco
Published: 28th, January 2025 GMT
Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Afirka CAF, ta fitar da jadawalin ƙasashen da za su fafata a Gasar Kofin Nahiyyar Afirka AFCON wadda Morocco za ta karɓi baƙunci a watan Disamba na bana.
An gudanar da bikin fitar da jadawalin ranar Litinin a Cibiyar Taro ta Ƙasa ta Mohammed V National da ke birnin Rabat a Morocco.
Tawagogi biyu mafi ƙwazo a kowanne rukuni ne za su tsallaka kai tsaye zuwa mataki na gaba, sai kuma tawagogi huɗu mafi ƙwazo da suka zo a mataki na uku a duk cikin rukunan.
Morocco wadda wannan shi ne karo na farko da za ta kasance mai masaukin baƙi tun 1988, za ta jagoranci rukunin A, inda za ta ɓarje gumi da Mali da Zambia da kuma Comoros.
Masar da ta taɓa lashe gasar sau bakwai a tarihi, za ta kara ne da Afrika ta Kudu da Angola da kuma Zimbabwe a rukunin B.
Rukunin C kuwa wanda ya ƙunshi Nijeriya wadda ta lashe kofin sau uku, za ta yi karon-batta da Tunisia da Uganda da kuma Tanzania.
Senega da ta lashe gasar a shekarar 2021, za ta kara da Jamhuriyar Dimukaraɗiyar Congo da Benin da kuma Botswana wacce wannan ne karo na biyu da za ta halarci gasar.
Algeria ce ke jagorantar rukunin E wanda ya ƙunshi ƙasashen Burkina Faso da Equatorial Guinea da Sudan.
Cote d’Ivoire wacce ke kare kambin ta na rukuni F, tare da Kamaru da Gabon da kuma Mozambique.
A dai ranar 21 ga watan Disamba ne za a buɗe gasar da karawa tsakanin Morocco da Comoros, sai kuma a buga wasan ƙarshe a ranar 18 ga watan Janairun 2026.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka
Bisa rahoton bunkasar hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da nahiyar Afirka na shekarar 2025, wanda aka gabatar a jiya Juma’a 13 ga wata, an ce a halin yanzu, an samu babban sauyi a tsarin ciniki tsakanin Sin da Afirka, an kuma kyautata tsarin zuwa mai shafar fannoni da dama, mai inganci, mai kunshe da fasahohin zamani, kana a nan gaba za a samu karin damar hadin gwiwarsu a fannonin masana’antu, da aikin noma, da sadarwa, da tattalin arziki ta yanar gizo, da ayyukan more rayuwa, da makamashi mai tsafta, da hada-hadar kudi da sauransu.
A matsayin daya daga cikin manyan nasarorin da aka cimma a gun bikin baje koli na tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Afirka karo na 4, an gabatar da rahoton ne a taron gabatar da shirye-shiryen ayyukan hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Afirka, wanda aka gudanar a wannan rana.
Rahoton ya yi bayanin cewa, a shekarun baya-baya nan, an fadada cinikayyar Sin da Afirka, yawan kudin cinikayyar kaya tsakaninsu a shekarar 2023 ya zarce dalar Amurka biliyan 280, kuma yawan kudin cinikin hidimomi a tsakaninsu a shekarar 2021 ya kai sama da dalar Amurka biliyan 41 da miliyan 866, kana an kyautata tsarin cinikinsu.
A daya bangaren kuma, yawan jarin da Sin ta zubawa Afirka ya karu, wanda yawancinsu suka shafi sha’anin gine-gine. Haka zalika, an samu nasarori a fannin gina ayyukan more rayuwa, da gudanar da ayyuka a fannonin sufuri, da wutar lantarki, da sadarwa, da madatsun ruwa da sauransu, da kuma yin hadin gwiwarsu a fannonin ba da ilmi, da aikin noma, da kiwon lafiya, da samun ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba da sauransu. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp