Jadawalin Gasar AFCON 2025 da za a fafata a Morocco
Published: 28th, January 2025 GMT
Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Afirka CAF, ta fitar da jadawalin ƙasashen da za su fafata a Gasar Kofin Nahiyyar Afirka AFCON wadda Morocco za ta karɓi baƙunci a watan Disamba na bana.
An gudanar da bikin fitar da jadawalin ranar Litinin a Cibiyar Taro ta Ƙasa ta Mohammed V National da ke birnin Rabat a Morocco.
Tawagogi biyu mafi ƙwazo a kowanne rukuni ne za su tsallaka kai tsaye zuwa mataki na gaba, sai kuma tawagogi huɗu mafi ƙwazo da suka zo a mataki na uku a duk cikin rukunan.
Morocco wadda wannan shi ne karo na farko da za ta kasance mai masaukin baƙi tun 1988, za ta jagoranci rukunin A, inda za ta ɓarje gumi da Mali da Zambia da kuma Comoros.
Masar da ta taɓa lashe gasar sau bakwai a tarihi, za ta kara ne da Afrika ta Kudu da Angola da kuma Zimbabwe a rukunin B.
Rukunin C kuwa wanda ya ƙunshi Nijeriya wadda ta lashe kofin sau uku, za ta yi karon-batta da Tunisia da Uganda da kuma Tanzania.
Senega da ta lashe gasar a shekarar 2021, za ta kara da Jamhuriyar Dimukaraɗiyar Congo da Benin da kuma Botswana wacce wannan ne karo na biyu da za ta halarci gasar.
Algeria ce ke jagorantar rukunin E wanda ya ƙunshi ƙasashen Burkina Faso da Equatorial Guinea da Sudan.
Cote d’Ivoire wacce ke kare kambin ta na rukuni F, tare da Kamaru da Gabon da kuma Mozambique.
A dai ranar 21 ga watan Disamba ne za a buɗe gasar da karawa tsakanin Morocco da Comoros, sai kuma a buga wasan ƙarshe a ranar 18 ga watan Janairun 2026.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki
Rundunar Sojojin Nijeriya (AFN) za ta gudanar da bikin kammala aiki na tsohon Shugaban Tsaron Ƙasa (CDS), Janar Christopher Gwabin Musa (mai ritaya) a ranar Jumma’a, 31 ga Oktoba, 2025, domin girmama ayyukan da ya gudanar a lokacin hidimarsa.
A cewar sanarwar da shalƙwatar tsaro ta ƙasa (DHQ) ta fitar a ranar Alhamis, an shirya bikin Pulling Out Parade ɗin ne da ƙarfe 09:00 na safe, inda manyan hafsoshin Soja, da jami’an gwamnati da ƴan uwa za su halarta. Wannan biki na nuni da kammala aikin Soja a matakin ƙoli, kuma yana ɗaya daga cikin manyan al’adun da ake yi wa manyan jami’an da suka yi aiki da ƙwarewa da sadaukarwa.
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP Kasashen Afirka Biyar Da Suka Fi Karfin SojiJanar Musa ya yi aikin Soja na tsawon shekaru masu yawa, kuma ya yi shugabanci a matsayin Shugaban Tsaron Ƙasa daga Yuni 2023 zuwa Oktoba 2025. A wannan lokaci, ya jagoranci manyan hare-haren yaƙi da ta’addanci tare da ƙarfafa hulɗar haɗin gwuiwa tsakanin sassan Sojojin Nijeriya.
A ranar 24 ga Oktoba, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sanar da sabon tsarin jagorancin rundunar Soja, inda ya naɗa Manjo Janar Olufemi Oluyede a matsayin sabon Shugaban Tsaro, wanda hakan ya kawo ƙarshen wa’adin Janar Musa.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA