Aminiya:
2025-08-02@00:54:28 GMT

Jadawalin Gasar AFCON 2025 da za a fafata a Morocco

Published: 28th, January 2025 GMT

Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Afirka CAF, ta fitar da jadawalin ƙasashen da za su fafata a Gasar Kofin Nahiyyar Afirka AFCON wadda Morocco za ta karɓi baƙunci a watan Disamba na bana.

An gudanar da bikin fitar da jadawalin ranar Litinin a Cibiyar Taro ta Ƙasa ta Mohammed V National da ke birnin Rabat a Morocco.

A soma duba watan Sha’aban ranar Laraba — Sarkin Musulmi Nijeriya na da arzikin da za ta riƙa ɗaukar nauyin tafiye-tafiyen Tinubu — Minista

Tawagogi biyu mafi ƙwazo a kowanne rukuni ne za su tsallaka kai tsaye zuwa mataki na gaba, sai kuma tawagogi huɗu mafi ƙwazo da suka zo a mataki na uku a duk cikin rukunan.

Morocco wadda wannan shi ne karo na farko da za ta kasance mai masaukin baƙi tun 1988, za ta jagoranci rukunin A, inda za ta ɓarje gumi da Mali da Zambia da kuma Comoros.

Masar da ta taɓa lashe gasar sau bakwai a tarihi, za ta kara ne da Afrika ta Kudu da Angola da kuma Zimbabwe a rukunin B.

Rukunin C kuwa wanda ya ƙunshi Nijeriya wadda ta lashe kofin sau uku, za ta yi karon-batta da Tunisia da Uganda da kuma Tanzania.

Senega da ta lashe gasar a shekarar 2021, za ta kara da Jamhuriyar Dimukaraɗiyar Congo da Benin da kuma Botswana wacce wannan ne karo na biyu da za ta halarci gasar.

Algeria ce ke jagorantar rukunin E wanda ya ƙunshi ƙasashen Burkina Faso da Equatorial Guinea da Sudan.

Cote d’Ivoire wacce ke kare kambin ta na rukuni F, tare da Kamaru da Gabon da kuma Mozambique.

A dai ranar 21 ga watan Disamba ne za a buɗe gasar da karawa tsakanin Morocco da Comoros, sai kuma a buga wasan ƙarshe a ranar 18 ga watan Janairun 2026.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba

Fira ministan Birtaniya ya bayyana cewa: Za su amince da kasar Falasdinu a watan Satumba idan yanayin Gaza bai canza ba

Keir Starmer ya kara da cewa, an dauki wannan matakin ne domin kare tsarin kasashe biyu, kuma kasarsa na da wani nauyi na musamman da ya rataya a wuyanta wajen ganin an samar da zaman lafiya a tsakanin kasashen biyu. Ya ce tallafin da kasarsa ke baiwa Tel Aviv yana nan daram.

Fira ministan na Burtaniya ya jaddada cewa kin amincewar da fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ya yi na samar da kasashe biyu kuskure ne kuma kuskure ne na dabi’a da dabaru.

Ya jaddada cewa dole ne a bude mashigar kasa sannan kuma a bar manyan motocin abinci 500 shiga Gaza a kullum rana.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami July 30, 2025 Faransa Ta Bayyana Wuce Gona Da Irin ‘Yan Sahayoniyya Kan Falasdinawa Da Ayyukan Ta’addanci July 30, 2025 Jagora: Iran Ta Bayyana Karfinta Da Jajircewarta A Yakin Kwanaki 12 Ga Duniya July 29, 2025 Mutum daya Yayi Shahada 4 Sun Ji Rauna Sanadiyar Hare-Haren HKI A Lebanon July 29, 2025 EU Tace Zata Dakatar Da HKI Daga Cibiyar Bincikenta Saboda Gaza July 29, 2025 Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar July 29, 2025 Najeriya: Likitoci a Lagas Sun Shiga Yajin Aiki July 29, 2025  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai July 29, 2025 Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu July 29, 2025  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta July 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Har yanzu ana fama da cutar kwalara a Najeriya – UNICEF
  • INEC za ta fara rajistar ƙuri’a a ranar 18 ga Agusta
  • Nijeriya Na Asarar Kusan Naira Tiriliyan 17.9 Duk Shekara Sakamakon Cutar Hanta — Gwamnati
  • Afirka ta Kudu na shirin daukar matakan kauce wa tasirin harajin Amurka
  • Peter Obi zai lashe jihohin Arewa idan ya koma PDP – Jerry Gana
  • Kananan Yan Wasan Dabben Gargajiya Na Iran Sun Zama Zakara A Gasar Wannan Shekara
  • Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United
  • Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa
  • Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka
  • Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba