Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-02@14:11:41 GMT

‘Yan Sanda Sun Kamu A Kano

Published: 28th, January 2025 GMT

‘Yan Sanda Sun Kamu A Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta samu gagarumar nasara wajen yaki da miyagun laifuka, inda ta kama wasu da ake zargi da aikata manyan laifuka da dama.

 

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Salman Dogo Garba ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar ‘yan sandan Bompai Kano.

 

Ya ce rundunar ta kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu wajen yin garkuwa da kuma kashe Alhaji Atiku Mu’azu, mai shekaru 64 da haihuwa mazaunin Janbulo, Kano.

 

Wadanda ake zargin, Abubakar Hassan (wanda aka fi sani da Captain), Adamu Abubakar Adam, da Alhaji Hamisu (wanda aka fi sani da Bakin Bross), an kama su ne bayan wani ci gaba da bincike da jami’an leken asiri suka yi.

 

A wani labarin kuma wasu ‘yan bindiga sun kai farmaki gidan Alhaji Auwalu da ke Sabuwar Unguwa Garo a karamar hukumar Kabo a Kano, inda suka yi masa fashin Naira miliyan 8 tare da yin garkuwa da ‘yarsa Zainab Aliyu mai shekaru 16.

 

CP Salman Dogo Garba ya ci gaba da cewa, ‘yan sanda sun fara gudanar da bincike domin ceto wanda aka kashe tare da damke wadanda suka aikata laifin.

 

Kwamishinan ‘yan sandan ya ci gaba da bayyana cewa, a wani samame na daban, rundunar ‘yan sandan ta kama wasu mutane 17 da ake zargin ‘yan fashi da makami ne da suka abkawa Hotoro a Kawo Kano, inda suka farfasa shaguna da motoci, tare da far wa mutanen da ba su ji ba ba su gani ba.

 

“An kuma kama wasu mutane uku da ake zargin ‘yan fashi da makami ne da laifin kai hari ga wasu mutane biyu da ba su ji ba ba su gani ba, tare da yi musu fashin wayoyin hannu guda 200 a unguwar Yankatsari da ke Kano.

 

CP Salman Dogo Garba ya bukaci jama’a da su kiyaye da taka tsantsan, kuma su kai rahoto ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa da su ko kuma ta lambobin hukumar: 08032419754, 08123821575, 09029292926.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Yansanda wasu mutane

এছাড়াও পড়ুন:

Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa

Madagascar ta sanar da kafa sabuwar gwamnati wadda ta kunshi fitattun ‘yan adawa guda uku a manyan mukamai na ministoci.

An gabatar da majalisar ministoci mai mambobi 29, wacce ta kunshi mata 10, a wani biki da aka gudanar a Fadar Gwamnatin Yavoloha da ke babban birnin kasar, Antananarivo.

Shugaban rikon kwarya Michael Randrianireina ya bayyana a lokacin bikin cewa manyan abubuwan da sabuwar gwamnatin ta sa gaba sun hada da yaki da rashin adalci, aiwatar da matakan tsuke bakin aljihu, da kuma samar da yanayin kasuwanci mai dorewa.

Ya kara da cewa kowane minista dole ne ya samar da sakamako mai kyau cikin watanni biyu, yana mai gargadin cewa rashin yin hakan a cikin wannan lokacin zai zama gazawa kuma zai iya haifar da maye gurbin minister a nan take.

An nada Christine Razanahasoa, tsohuwar Ministar Shari’a kuma tsohuwar Kakakin Majalisar Dokoki ta Kasa, a matsayin Ministar Harkokin Waje, kuma an nada Fanerisoua Irinavo, tsohuwar alkali wacce ta dawo daga gudun hijira daga  Faransa, a matsayin Ministar Shari’a.

An nada Hanitra Razavimanantsoa, ​​’yar majalisa daga jam’iyyar Tiaco Madagascar karkashin jagorancin tsohon shugaban kasar Marc Ravalomanana, a matsayin Ministar Kasa a ma’aikatar Sake Gina Kasa. Waɗannan mutane uku suna wakiltar muryoyin  manyan bangarorin ‘yan adawa a Madagascar.

Jagoran juyin mulkin, Michel Randrianireina, ya kwace mulki a ranar 14 ga Oktoba bayan tsohon shugaban kasar Andry Rajoelina ya tsere daga kasar a cikin jirgin saman sojojin Faransa bayan makonni na zanga-zanga.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran ta yi fatali da kalamman IAEA Kan Shirin Nukiliyarta October 30, 2025 Trump Ya Umarci Ma’aikatar Yakin Amurka Ta koma gwajin makaman nukiliya October 30, 2025 Isra’ila ta amince da fadada matsugunai a Yammacin Kogin Jordan October 30, 2025 Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu October 30, 2025 Sudan : Kasashen duniya na tir da cin zarafi a El-Fasher October 30, 2025 Iran Ta Jaddada Bin Hanyar Diflomasiya Ko Da A Lokacin Yaki Ne Amma Ba Zata Amince Da Bin Umarni Ba October 30, 2025 Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri October 30, 2025 Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin October 30, 2025 Kungiyar Rapid Support Forces Ta Sanar Da Kafa Kwamitin Bincike Kan Cin Zarafin Al’umma A El Fasher October 30, 2025 An Kafa Dokar Ta Baci A Darul-Salam Saboda Tarzoman Zaben Shugaban Kasa A Tanzania October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa
  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara