Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-09-18@01:13:45 GMT

‘Yan Sanda Sun Kamu A Kano

Published: 28th, January 2025 GMT

‘Yan Sanda Sun Kamu A Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta samu gagarumar nasara wajen yaki da miyagun laifuka, inda ta kama wasu da ake zargi da aikata manyan laifuka da dama.

 

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Salman Dogo Garba ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar ‘yan sandan Bompai Kano.

 

Ya ce rundunar ta kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu wajen yin garkuwa da kuma kashe Alhaji Atiku Mu’azu, mai shekaru 64 da haihuwa mazaunin Janbulo, Kano.

 

Wadanda ake zargin, Abubakar Hassan (wanda aka fi sani da Captain), Adamu Abubakar Adam, da Alhaji Hamisu (wanda aka fi sani da Bakin Bross), an kama su ne bayan wani ci gaba da bincike da jami’an leken asiri suka yi.

 

A wani labarin kuma wasu ‘yan bindiga sun kai farmaki gidan Alhaji Auwalu da ke Sabuwar Unguwa Garo a karamar hukumar Kabo a Kano, inda suka yi masa fashin Naira miliyan 8 tare da yin garkuwa da ‘yarsa Zainab Aliyu mai shekaru 16.

 

CP Salman Dogo Garba ya ci gaba da cewa, ‘yan sanda sun fara gudanar da bincike domin ceto wanda aka kashe tare da damke wadanda suka aikata laifin.

 

Kwamishinan ‘yan sandan ya ci gaba da bayyana cewa, a wani samame na daban, rundunar ‘yan sandan ta kama wasu mutane 17 da ake zargin ‘yan fashi da makami ne da suka abkawa Hotoro a Kawo Kano, inda suka farfasa shaguna da motoci, tare da far wa mutanen da ba su ji ba ba su gani ba.

 

“An kuma kama wasu mutane uku da ake zargin ‘yan fashi da makami ne da laifin kai hari ga wasu mutane biyu da ba su ji ba ba su gani ba, tare da yi musu fashin wayoyin hannu guda 200 a unguwar Yankatsari da ke Kano.

 

CP Salman Dogo Garba ya bukaci jama’a da su kiyaye da taka tsantsan, kuma su kai rahoto ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa da su ko kuma ta lambobin hukumar: 08032419754, 08123821575, 09029292926.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Yansanda wasu mutane

এছাড়াও পড়ুন:

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 

Yarjejeniyar, a cewar daukacin mahalarta taron, ta nuna wani gagarumin mataki na kawo karshen tashe-tashen hankula, garkuwa da mutane da satar shanu a Arewa maso Yamma, da kuma yankin Arewa.

 

Yarjejeniyar wacce Mai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi, da shugaban karamar hukumar, Babangida Abdullahi Kurfi suka shirya, ta gudana ne a dajin Wurma, inda ake fama da rashin tsaro.

 

Manyan jagororin ‘yan bindigan da suka hada da Alhaji Usman Kachalla Ruga da Sani Muhindinge da Yahaya Sani (Hayyu) da kuma Alhaji Shu’aibu duk sun yi alkawarin tsagaita wuta.

 

Daga baya suka sako mutanen da suka kama kuma suka bar manoma su koma gonakansu ba tare da wata barazana ba.

 

Sai dai kasa da wata guda da kulla yarjejeniyar, an tattaro cewa ‘yan bindigar sun sake kai hari a Zamfara inda suka yi awon gaba da masallata da dama.

 

Wata majiya ta cikin garin, ta shaida cewa, harin ya afku ne a lokacin sallar asuba da misalin karfe 5:30 na safe, inda ‘yan bindigar suka afkawa masallacin, suka kewaye shi, sannan suka tattara masallatan zuwa daji.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000