Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-06-15@08:06:36 GMT

‘Yan Sanda Sun Kamu A Kano

Published: 28th, January 2025 GMT

‘Yan Sanda Sun Kamu A Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta samu gagarumar nasara wajen yaki da miyagun laifuka, inda ta kama wasu da ake zargi da aikata manyan laifuka da dama.

 

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Salman Dogo Garba ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar ‘yan sandan Bompai Kano.

 

Ya ce rundunar ta kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu wajen yin garkuwa da kuma kashe Alhaji Atiku Mu’azu, mai shekaru 64 da haihuwa mazaunin Janbulo, Kano.

 

Wadanda ake zargin, Abubakar Hassan (wanda aka fi sani da Captain), Adamu Abubakar Adam, da Alhaji Hamisu (wanda aka fi sani da Bakin Bross), an kama su ne bayan wani ci gaba da bincike da jami’an leken asiri suka yi.

 

A wani labarin kuma wasu ‘yan bindiga sun kai farmaki gidan Alhaji Auwalu da ke Sabuwar Unguwa Garo a karamar hukumar Kabo a Kano, inda suka yi masa fashin Naira miliyan 8 tare da yin garkuwa da ‘yarsa Zainab Aliyu mai shekaru 16.

 

CP Salman Dogo Garba ya ci gaba da cewa, ‘yan sanda sun fara gudanar da bincike domin ceto wanda aka kashe tare da damke wadanda suka aikata laifin.

 

Kwamishinan ‘yan sandan ya ci gaba da bayyana cewa, a wani samame na daban, rundunar ‘yan sandan ta kama wasu mutane 17 da ake zargin ‘yan fashi da makami ne da suka abkawa Hotoro a Kawo Kano, inda suka farfasa shaguna da motoci, tare da far wa mutanen da ba su ji ba ba su gani ba.

 

“An kuma kama wasu mutane uku da ake zargin ‘yan fashi da makami ne da laifin kai hari ga wasu mutane biyu da ba su ji ba ba su gani ba, tare da yi musu fashin wayoyin hannu guda 200 a unguwar Yankatsari da ke Kano.

 

CP Salman Dogo Garba ya bukaci jama’a da su kiyaye da taka tsantsan, kuma su kai rahoto ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa da su ko kuma ta lambobin hukumar: 08032419754, 08123821575, 09029292926.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Yansanda wasu mutane

এছাড়াও পড়ুন:

Ƙwazo da juriya suka sa na zura ƙwallaye 10 a wasanni 10 – Mane

Sadeeƙ Umar da ake yi wa laƙabi da Mane, matashin ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne da yake tashen taka leda a rukunin ’yan dagaji a Jihar Kano.

Matashin, wanda tauraronsa ke haskawa a fagen tamola ya yi fice ne bayan da ya kafa wani sabon tarihi na zura ƙwallaye 10 a raga a wasanni 10 da ya buga tare da ba da taimako sau 6 wajen wasu ƙwallayen a rukuni gasar wasannin ’yan dagaji aji 1 da aka fi sani da Amateur 1 a Jihar Kano.

An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa

A cikin tattaunawarsa da Aminiya, Sadeeƙ Mane ya bayyana cewa, ƙwazo da sadaukar da kai ne suka taimaka masa wajen kafa wanna tarihi.

Sadeeƙ, wanda kamar sauran ‘yan wasa ya fara buga ƙwallon ne a cikin unguwa kafin daga bisani ya fara buga wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Togo da ke Unguwar Birget, Ƙaramar Hukumar Nasarawa a Jihar Kano.

Daga ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Togo, Sadeeƙ ya koma taka leda a ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Legend FC, inda a can ne bayan ya nuna bajinta a Gasar Cin Kofin Shugaban Ƙaramar Hukumar Nasarawa, Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta SBS Waliyya da ke buga wasa a matakin Amauteur 1 ta ɗauke shi.

A kakar bana Saƙeeƙ ya kafa tarihi, inda ya buga wasanni goma kuma ya zura ƙwallaye goma a raga.

Wannan nasara da ya samu ta sa ya lashe kyautar ɗan wasan da ya fi kowanne ɗan wasa zura ƙallaye a raga a wannan shekara.

Haka kuma an zaɓi Saƙeed a matsayin ɗan wasan da ya fi kowanne ɗan wasa ƙwarewa a wannan matakin.

Da yake ƙarin bayani kan yadda ya samu nasarar zura ƙwallaye 10 a cikin wasanni 10, Sadeeƙ ya ce, “na buga wasanni 10 kuma na zura ƙwallaye 10 a ragar abokan karawa.

A cikin wasanni 10 ɗin na zura ƙwallayen ne a wasanni 8, wato wasa 2 kacal ne ban ci ƙwallo ba. Wannan ne ya sa na zama ɗan wasan da ya fi zura ƙwallo a gasar.”

Da yake amsa tambayar ko me ne sirrin wannan nasarori haka?

Sadeeƙ Umar sai ya ce: “Ka san an ce in ka ji wane ba banza ba, wato in ba a sha gumi ba a sha rana. Don haka na jajirce ne da ba wa kaina horo da kuma sanya juriya a zuciyata. Wato ina nufin bayan horon da ake yi mana a filin wasa, ni a karan kaina ina fita, in yi gudu da dadare da sauran wasanni na motsa jiki masu wahala don in saba wa kaina,” in ji Mane.

Ya ƙara da cewa, “wannan shi ya sa za ka ga in na shiga fili bana gajiya har a tashi. Haka kuma, wannan shi ne dalilin da ya sa ake yi min laƙabi da shahararren ɗan wasan ƙasar Senegal ɗin nan mai suna Sadio Mane, wato ganin irin salon wasanmu ɗaya ne, kai har ma wasu na cewa, wai mun yi kama ko a fuska.”

Sadeeƙ Mane ya bayyana wa Aminya cewa, burinsa shi ne wata rana ya zama kamar Sadio Mane wato ya fita ƙasashe Turai, ya buga wa manyan ƙungiyoyin ƙwallo ƙafa na duniya wasa.

“Kamar kowane matashin ɗan ƙwallo, ni ma babban burina shi ne in buga ƙwallo a ƙasashen Turai, in shahara kamar Sadio Mane. Ina ji a raina wata rana zan buga wa manyan ƙungiyoyi kamar Chealsea da Liɓerpool da Barcelona,” in ji matashi ɗan wasan.

Sai dai Sadeeƙ ya bayyana cewa, ba kamar sauran matasan ’yan ƙwallo ba da suke son shiga Turai gaba-gaɗi, shi yana da burin ya buga wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars kafin ya tafi ƙasashen Turai da ƙwallo.

“A gaskiya ni in so samu ne, na fi son in fara buga wa Kano Pillars wasa kafin in je Turai. Saboda tunda na taso, ina son Pillars sosai. Haka kuma ina ga a matsayina na ɗan Kano zai zamo abin alfahari a gare ni a ce wata rana na sanya wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillar riga, na ba da tawa gudunmawar,” in ji Mane.

Mane ya bayyana rashin samun haɗuwa da manajan masu ɗaukar matasan ‘yan wasa zuwa ƙasashen Turai, musamman a jihohin Arewa a matsayin wani babban ƙalubale da matasan ‘yan wasa masu hazaƙa ke gamuwa da shi a wannan yanki.

“Babban ƙalubalenmu a nan Kano da sauran jihohin Arewa shi ne wa zai taimake ka, ya haɗa kai da manajan da suke ɗaukar matasan ‘yan wasa zuwa Turai. Ka ga muna da matasa masu ƙwazo da basira sosai, sai dai ba ma samun wannan gatan. Ban san dalilin da ya sa manajojin ɗin ba sa son zuwa nan ba,” In ji Sadeeƙ Mane.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Ƙwazo da juriya suka sa na zura ƙwallaye 10 a wasanni 10 – Mane
  • EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna