Kungiyar “ISWAP” Ta Kashe Sojojin Najeriya 20
Published: 27th, January 2025 GMT
A kalla sojojin Najeriya 20 ne su ka kwanta dama daga cikinsu har da kwamanda a wani hari da ake dangantawa kungiyar ‘yan ta’adda ta ISWAP.
‘Yan ta’addar sun kai harin ne dai a ranar Juma’ar da ta gabata a kan sansanin bataliya ta 146 dake Malam-Fatori a akan iyakar Najeriya da Nijar a jihar Borno.
Wani soja da ya tsira daga wannan harin ya fadi cewa harin ‘yan ta’addar ya dauki sa’oi 3, kuma sun je wurin ne a cikin manyan motoci tare da shammatar sojojin.
Kamfanin dillancin labarun Reuters wanda ya ambato sojan ya ce, maharan sun rika harbinsu ta kowace kusurwa, sai dai sun mayar da wuta.Haka nan kuma ya tabbatar da cewa an kashe kwamandnsu.
Mazaunan yankin da aka kai harin sun tabbatar da cewa maharan sun kone gine-gine masu yawa, da ya tilastawa mazauna yankin yin hijira.
Haka nan kuma an tabbatar da cewa har zuwa Asabar da dare an rika ganin maharan a cikin wannan yankin suka karakaina.
Ita dai kungiyar “ISWAP” ta balle ne daga Bokoharam a 2016, kuma tana kai wa sojoji da jami’an tsaron Najeriya hare-hare. A tsawon shekaru 15 na hare-haren ‘yan ta’adda a wannan yankin mutane kusan 40,000 ne su ka kwanta dama,wasu miliyan biyu kuwa su ka tarwatse.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Limamin Masallacin Jumma’a A Nan Tehran Ya Yi Magana Dangane Da Kwatar Garin Khurramshar Daga Sojojin Sadam
Mataimakin limamin Jumma’a a nan Tehran Sheikh kum Hujjatul Islam Kazen Sadiki bayan yayio Magana a kan al-amuran tsaron All..da kuma yadda bayin All..da kuma shidanun mutane zasu mutu da kuma yadda sakamakon ko wannansu a gaban All…/ Ya kuma ya gamanar fatahin garin KharramShahr dake kudancin kasar Iran kuma kan iyaka da kasar Iran, wanda dakarun kare juyin juya halin musulunci tare da sauran sojoji da mayakan sa kai suka kwace wannan garin daga hannun sojojin Sdam Hussain a rana irin ta yau wato 2 ga watan Khordod.
Banda haka lamamin yana Magana kan littafan da aka buga dangane da wannan gagarumin fatahin da mutanen Iran suka sami a kan wannan garin. Wanda kuma daga wannan nasarar ne ta ci gaba da samun nasara har aka kawo karshen yakin a shekara 1988M.