HausaTv:
2025-05-02@05:00:04 GMT

Lebanon: Mutanen Kudancin Lebanon Suna Ci Gaba Da Kowama Garuruwansu

Published: 27th, January 2025 GMT

A rana ta biyu a jere, mutanen kudancin Lebanon suna ci gaba da komawa gururwansu da kauyukansu duk da hare-haren da Isra’ila take kai musu.

Tashar talabijin din “almayadin” mai watsa shirye-shiryenta daga kasar Lebanon ta ce, jirgin Isra’ila maras matuki,ya jefa bom din sauti na tsorata mutanen da suke komawa garuruwan nasu ,musamman a gefen garin Lamisul-Jabal, domin hana su shiga.

Mutanen garin sun ce za su shiga garin nasu ko da kuwa za su yi shahada ko kuma su jikkata.

Haka nan kuma sojojin na HKI sun kai farmaki akan sojojin Lebanon da suka taru a yankin al-Mafilah.

Ma’aikatar kiwon lafiya ta Lebanon ta sanar da cewa, mutane biyu sun jikkata sanadiyyar hare-haren na HKI a yau Litinin.

A jiya Lahadi ne dai wa’adin kwanaki 60 daga kare yakin Lebanon ya cika, da yarjejeniyarsa ta kunshi ficewar sojojin HKI daga garuruwan da su ka yi kutse.

Sai dai sojojin na mamaya sun ki ficewa, da hakan ya sa mutanen kudancin Lebanon su ka kutsa cikin garuruwan nasu. A kalla mutane 22 ne su ka yi shahada a jiya da kuma jikkata wasu masu yawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Tatsuniya wata hanya ce ta ilmantarwa da bayar da tarbiyya da kuma koyar da al’adu da halaye na gari a tsakanin Hausawa.

Tatsuniyoyi na ɗauke da darussa na rayuwa, suna kuma koya wa yara da manya jarumta da tausayi da sauran dabi’u kyawawa.

Sai dai a yayin da duniya take sauyawa, ba kasafai matasa suke sha’awar sauraron tatsuniya ba.

NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa

Wannan ne batun da shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka ta sake kai Hari a yankunan Saada da Hudaidah na Yemen
  • Gwamnatin Jihar Za Ta Ci Gaba Da Bullowa Da Dubarun Bunkasar Ta
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta
  • Dubban Mutanen Burkina Faso Sun Yi  Gangamin Nuna Goyon Bayan Shugaban Kasa Ibrahim Traore
  • Munafunci Dodo Ya Kan Ci Mai Shi
  • DAGA LARABA: Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Quneitra Na Kasar Siriya Tare Da Kafa Shingen Bincike
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
  • Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno