HausaTv:
2025-08-01@09:57:45 GMT

Lebanon: Mutanen Kudancin Lebanon Suna Ci Gaba Da Kowama Garuruwansu

Published: 27th, January 2025 GMT

A rana ta biyu a jere, mutanen kudancin Lebanon suna ci gaba da komawa gururwansu da kauyukansu duk da hare-haren da Isra’ila take kai musu.

Tashar talabijin din “almayadin” mai watsa shirye-shiryenta daga kasar Lebanon ta ce, jirgin Isra’ila maras matuki,ya jefa bom din sauti na tsorata mutanen da suke komawa garuruwan nasu ,musamman a gefen garin Lamisul-Jabal, domin hana su shiga.

Mutanen garin sun ce za su shiga garin nasu ko da kuwa za su yi shahada ko kuma su jikkata.

Haka nan kuma sojojin na HKI sun kai farmaki akan sojojin Lebanon da suka taru a yankin al-Mafilah.

Ma’aikatar kiwon lafiya ta Lebanon ta sanar da cewa, mutane biyu sun jikkata sanadiyyar hare-haren na HKI a yau Litinin.

A jiya Lahadi ne dai wa’adin kwanaki 60 daga kare yakin Lebanon ya cika, da yarjejeniyarsa ta kunshi ficewar sojojin HKI daga garuruwan da su ka yi kutse.

Sai dai sojojin na mamaya sun ki ficewa, da hakan ya sa mutanen kudancin Lebanon su ka kutsa cikin garuruwan nasu. A kalla mutane 22 ne su ka yi shahada a jiya da kuma jikkata wasu masu yawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina

An ceto dukkanin mutane 14 ba tare da wani ya ji rauni ba, amma abin baƙin ciki, wani matashi ɗan shekara 27 mai suna Abba daga garin Funtua ya rasa ransa kafin isowar ’yansanda.

A wani lamari da ya faru a ranar 28 ga watan Yuli da misalin ƙarfe 11:27 na dare, an sake kiran ’yansanda daga ƙauyen Zagaizagi, inda aka sanar da su cewa wasu ’yan bindiga sum hari tare da sace wasu mutane ƙauyen.

’Yansanda sun isa wajen suka gwabza da ’yan bindigar, kuma sun samu nasarar ceto wasu mutane 14 da kuma ƙwato shanun da aka sace guda biyu.

Amma, mutane biyu daga cikin mazauna ƙauyen sun rasa rayukansu a harin.

Rundunar ta ce har yanzu tana ci gaba da ƙoƙarin kamo ’yan bindigar da suka tsere.

Kwamishinan ’yansandan, CP Bello Shehu, ya yaba wa jami’ansa bisa jarumtaka da suka nuna.

Ya kuma buƙaci jama’a da su ci gaba da bai wa ’yansanda sahihan bayanai a kan lokaci.

Ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Shugaban Kasar Lebanon Aun Ya Ce Mun Aike Wa  Amurka Sakwanni Akan Dakatar Da Hare-haren HKI
  •  Sojojin Sahayoniya Suna Ci Gaba Da Kisan Kiyashi A Gaza
  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura
  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Yadda ’yan bindiga suka tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • ’Yan bindiga sun tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu