Jagora: An Murkushe Dukkanin Daidaito A Gaban Mutanen Kudancin Kasar Lebanon
Published: 27th, January 2025 GMT
Jagoran juyin juya halin Musulunci: An murkushe dukkanin daidaito a gaban mutanen kudancin Lebanon
Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya bayyana abin da ya faru a kudancin kasar Lebanon a matsayin murkushe dukkanin daidaito na siyasa da lissafin abin duniya.
A cikin wani rubutu a dandalin “X”, Ayatullahi Sayyid Khamenei ya nuna cewa an murkushe wadannan daidaito a gaban mutane masu aminci da aminci a kudancin Lebanon.
Jagoran juyin juya halin Musulunci ya yi la’akari da cewa: Al’ummar kudancin kasar Labanon ba su damu da sojojin yahudawan sahayoniyya da suka yi kaca-kaca da su ba, suna kuma kai rayukansu zuwa fagen fama da rashin son kai da kuma dogaro da alkawarin Ubangiji.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Birgediya Pakphur: Nan Gaba Kadan Za A Budewa “Isra’ila” Kofofin Jahannama
Sabon kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran Birgadiya Muhammad Pakphur ya aike wa da jagoran juyin musulunci na Iran wasika da a ciki ya bayyana cewa:
” Laifukan ta’addanci da HKI ta aikata, wanda ya yi sanadiyyar shahadar manyan kwamandojin da kuma malaman Nukiliya, haka nan mata da kananan yara da ba su ji ba su gani ba, ba zai wuce ba tare da mayar da martani ba.”
Bugu da kari sabon kwamandan dakarun kare juyin musuluncin ya ce; Ba da jimawa ba, Za a buwa wa wannan haramtacciyar kasa kofofin jahannama.”
Birgeriya Muhamad Pakphur ya kuma kaddamar da ta’aziyya da kuma taya murnar shahadar kwamandojin, ya kuma yi godiya ga jagora da ya gaskata dakarun juyin.
Har ila yau Birgediya Pakphur Muhammad ya ce; Abinda ‘yan sahayoniyar su ka yi, wuce gona da iri ne da keta hurumin tsaron kasar Iran da zaman lafiyar jamhuriyar ta Iran, don haka ba zai wuce ba tare da mayar da martani ba.
Haka nan kuma ya ce: Kamar yadda jagoran juyin musulunci na Iran ya yi alkawali, wannan haramtacciyar kasar za ta fuskanci bakar makomarta da kuma mummunan sakamako.”
Wani sashe na wasikar sabon kwamandan dakarun kare juyin musuluncin na Iran ya kunshi cewa; Bisa dogaro da Allah, da kuma cika alkawalin da jagora ya yi, sannan kuma da daukar fansar jinanen shahidai kwamandoji, da masana da ‘yan kasa da ba su ji ba su gani ba, za a buewa wannan haramtacciyar kasa kofofin jahannama ba da jimawa ba.”