An gurfanar da masoyan da suka kai wa malami hari a Kano
Published: 26th, January 2025 GMT
Wata ɗaliba daga Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, mai suna Khadija Hassan Chiranchi, da kuma saurayinta Khalid Hussain wanda aka fi sani da Baffa, sun gurfana a gaban kotun Shari’ar Musulunci kan zargin kai wa malami hari.
Rahotanni sun bayyana cewa, Khadija ta gayyato saurayinta Khalid zuwa ofishin malamin, Aliyu Hamza Abdullahi, wanda ta ce yana zame mata matsala a karatunta.
A lokacin ne saurayin ya zaro adda ya sari malamin a kai.
Dukkaninsu sun gurfana a kotu kan tuhume-tuhumen da suka haɗa da, haɗa baki, aikata daba, kutse da cin zarafi.
Sun musanta zargin da ake musu, inda suka ce kotun ba ta da hurumin sauraron shari’ar.
Duk da haka, alƙalin kotun ya bayar da umarnin a tsare su a gidan yari har zuwa ranar 27 ga Fabrairu, 2025, don sake gurfanar da su.
Sai dai kuma, an zargi saurayin da mallakar makami mai hatsari, wanda ya amince da laifin.
Wanda a nan ne kotun ta ce tana da hurumin sauraron wannan ɓangaren na zargin, wanda ya sa aka ɗage shari’ar zuwa wannan rana domin ci gaba da sauraron ta.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
Shugaban aksar Iran, Massoud Pezeshkian, ya bayyana cewa martanin sojojin kasarsa ga Isra’ila zai zama mafi muni idan hare-haren Isra’ilar suka ci gaba.
A wata tattaunawa ta wayar tarho da firaministan Pakistan Shehbaz Sharif, shugaban kasar Iran Massoud Pezeshkian ya tabbatar da cewa dakarun gwamnatin Jamhuriyar Musulunci ta Iran za su dauki kwararan matakan mayar da martani mai tsauri idan har gwamnatin Isra’ila ta ci gaba da kai farmaki kan Iran.
“Masu da’awar kare hakkin bil’adama ba wai kawai suna goyon bayan zaluncin gwamnatin sahyoniyawa ba ne, har ma suna karfafa mata gwiwar aikata wadannan munanan ayyuka ta hanyar ba ta makamai da kayan aiki,” in ji shi.
Mr. Pezeshkian ya kara da cewa gwamnatin Isra’ila da ke samun goyon bayan Amurka da kasashen yammacin Turai ta sabawa dukkanin dokokin kasa da kasa.
A nasa bangaren, firaministan Pakistan ya bayyana goyon bayan kasarsa ga al’ummar iran, yana mai yin Allah wadai da keta hurumin kasar Iran da ‘yancinta, wanda ya zama cin zarafi ga dokokin kasa da kasa da kuma kundin tsarin mulkin MDD.
Sharif ya sake jaddada cewa Iran na da cikakken ‘yancin kare kanta a karkashin doka ta 51 na kundin tsarin mulkin MDD inda ya bayyana fatan ganin an dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.