Aminiya:
2025-09-18@00:57:03 GMT

An gurfanar da masoyan da suka kai wa malami hari a Kano

Published: 26th, January 2025 GMT

Wata ɗaliba daga Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Kano, mai suna Khadija Hassan Chiranchi, da kuma saurayinta Khalid Hussain wanda aka fi sani da Baffa, sun gurfana a gaban kotun Shari’ar Musulunci kan zargin kai wa malami hari.

Rahotanni sun bayyana cewa, Khadija ta gayyato saurayinta Khalid zuwa ofishin malamin, Aliyu Hamza Abdullahi, wanda ta ce yana zame mata matsala a karatunta.

Kotu ta ɗaure matashi shekara 2 kan satar wayoyi a Kano Karya ta kai kwikwiyonta mara lafiya asibiti

A lokacin ne saurayin ya zaro adda ya sari malamin a kai.

Dukkaninsu sun gurfana a kotu kan tuhume-tuhumen da suka haɗa da, haɗa baki, aikata daba, kutse da cin zarafi.

Sun musanta zargin da ake musu, inda suka ce kotun ba ta da hurumin sauraron shari’ar.

Duk da haka, alƙalin kotun ya bayar da umarnin a tsare su a gidan yari har zuwa ranar 27 ga Fabrairu, 2025, don sake gurfanar da su.

Sai dai kuma, an zargi saurayin da mallakar makami mai hatsari, wanda ya amince da laifin.

Wanda a nan ne kotun ta ce tana da hurumin sauraron wannan ɓangaren na zargin, wanda ya sa aka ɗage shari’ar zuwa wannan rana domin ci gaba da sauraron ta.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar

Antoni Janar na Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke birnin Yamai a Nijar, ya bayyana cewa an kama tsohon Ministan Harkokin Waje, Ibrahim Yacoubou, bisa zargin hannunsa a cikin wata aika-aika ta kisan kai domin yin tsafi.

A cewar Maazou Oumarou, lamarin ya samo asali ne daga wani binciken ’yan sanda da aka fara gudanarwa tun a ranar 29 ga Yuli, 2025.

KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja

Ya bayyana cewa, an soma gudanar da binciken ne dangane da yunƙurin kisa a wani yanki da ke wajen birnin Yamai, lamarin da ya kai ga cafke ababen zargin a garin Dosso.

Wani mutum mai suna Mahamadou Noura ne ya bayyana cewa shi ne ya yi yunƙurin kisan, tare da wasu kashe-kashe guda shida da ya aiwatar a baya, bisa umarnin wasu mutane, ciki har da tsohon ministan Ibrahim Yacoubou.

Mutumin ya shaida wa mahukunta cewa ya aikata hakan ne domin yin tsafi da gawarwakin, a madadin wasu mutane da suka haɗa da: Issa Ali Maiga da Ismael Morou Karama da Elhadji Bilya da kuma Issa Seybou Hama.

TRT ya ruwaito cewa tuni dai an cafke duk ababen zargin, yayin da Kotun Ɗaukaka Ƙarar ta umurci ’yan sanda da su ci gaba da bincike tare da ɗaukar ƙarin matakan da za su tabbatar da gaskiya.

Sanarwar ta ce: “Manufar wannan mataki na shari’a ita ce a tattara cikakken rahoto da ke ƙunshe da dukkan abubuwan da suka faru, sannan a miƙa shi ga ɓangaren gurfanarwa.”

Mai shigar da ƙara a ɓangaren gwamnati ya ce, la’akari da girman wannan lamari, wajibi ne a gudanar da bincike cikin gaggawa.

Haka kuma ya buƙaci al’umma da su mutunta ’yancin kotu tare da bayar da cikakken goyon baya domin fayyace gaskiya.

Ana iya tuna cewa, Ibrahim Yacoubou na daga cikin manyan jami’an da aka kama bayan juyin mulkin Nijar na ranar 26 ga Yuli, 2023, sai dai daga bisani an ba shi beli na wucin gadi a cikin watannin baya.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Ma’aikatar Shari’ar Iran Ta Sanar Da Rataye Dan Leken Asirin Hukumar Mossad Ta Isra’ila
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaidai Dake Kasar Yamen
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar