Kazalika, masu sukar na ganin cewa, gwamnatin ta yi watsi da irin halin ƙuncin rayuwa da musamman
talakwan ƙasar, ke ci gaba da fuskanta, kamar dai, na ci gaba da hauhawan farashin kayan masarufi da
ƙarin kuɗin Man Fetur da ƙarin kuɗin wutar lantarki da ƙarancin albashin da ake biyan ma’aikata,
musamman na gwamnati, wanda a baya, ta yi alƙawarin lalubo masu da mafita.

Wannan batun na ƙarin albashin, tamkar dai wani cin zarafi wanda kuma abu ne, da ke tattare da hatsari.
Kusan tun lokacin da shugaba Bola Tinubu, ya ɗare Karagar shugabancin ƙasar, ya rage yawan kuɗaɗen
da ake kashewa, na gudanar da mulki, inda gwamtainsa, ta rage yawan ɗimbin tawagar da take kwasa, na
yin tafiye-tafiye, musamman zuwa ƙasashen duniya.
Amma batun na ƙarawa ƴ an siyasa masu riƙe da madafun ikon, a wannan yanayin da ƙasar ke a ciki,
tamkar mayar da Agogo baya ne.
Misali, gwamnatin har zuwa yau, ta gaza wajen cika ɗaukacin buƙatun ƙungiyoyin manyan makaratun
ƙasar wato ASU da kuma ASUP, inda kuma a gefe ɗaya, ƙungiyoyin ƙwarrun likitoci, suma suke ta kai
gwauro da mari, na neman gwamnatin, ta biya masu na su buƙatun
Saboda rashin biya masu buƙatun na su, suke tsunduma cikin yajin aiki na gargaɗi ko kuma gargaɗi.

Hakazalik, a yayin da ƙasar ke jigelon kashe kuɗaɗe, na gudanar da wasu ayyuka a ƙetare, amma a gife
ɗaya, an bar ma’aikata na karɓar mafi ƙarancin alabshin na Naira 70,000 kacal, inda wannan kuɗin, ba zai
iya kawar masu koda da ƙishirwarsu ba, duba da hauhawan kayan masarufi, da ake ci gaba da fuskanta a
ƙasar.

Akasarin ma’aikata a ƙasar, na ci gaba da kasance wa ne a cikin talauci, inda kuma sauran ƴ an siyasa, ke
ci gaba da yin wadaƙa.
Maimakon ƙarin albashin kamata yi Hukumar ta fara tunanin fara yiwa albashin ma’aikatan gwamnati
garanbawul da kuma inganta rayuwarsu.A yayin da ƙasar ke ci gaba da fuskantar ƙaranci kuɗi tare da kuma yadda alummar ƙasarke ci gaba da
fitar da rai ga alƙawarin da gwamnatin shugaba Tinubu ta yi, na saita ƙasar, batun na yin ƙarin, a wannan
lokacin, wani abin dubawa ne.
Wannna Jaridar ta nuna takaicinta kan wannan batun, musamman duba da cewa, yunƙurin na Hukumar,
na ci gaba da fuskantar suka.

Bugu da ƙari, duba da cewa, Nijeriya kusan ta dogara ne kachokam, kan ciwao bashi daga ƙetare, domin
ci giɓin da take da shi, a cikin kasafin kuɗinta, wanda hakan ya saɓawa ƙa’ida, a saboda haka, batun na
ƙarin albashin ga ƴ an siyasa, tamkar zuba kuɗi ne, a inda bai kamata ba.
Ya zama wajibi, gwamnatin ta dakatar da wannan batun na ƙarin albashin ga ƴ an siyasa masu riƙe da
madafun iko, amma ta mayar da hankali, wajen gudanar da bin diddigin kashe kuɗaɗe wanda zai yi daidai
da, tsarin tattalin arzikin ƙasar, a zahirance da kuma gudanar da ƙa’idojin gudanar da aikin gwamnati.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Siyasa ƙarin albashin ƴ an siyasa

এছাড়াও পড়ুন:

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

A bayan bayan nan, an aiwatar da jerin tattaunawa tsakanin Sin da Amurka karkashin jagorancin shugabanninsu, inda aka samu kyawawan sakamakon da ya kyautata alakarsu ta tattalin arziki da cinikayya. Wannan ya nuna shawarar da a kullum Sin ke bayarwa cewa, tattaunawa ita ce mafita ga dukkan rikice-rikice, maimakon amfani da karfi.

Kasar Sin ta sha nanata cewa, babu mai samun nasara a yakin cinikayya ko haraji. Mun ga yadda aka samu hauhawar farashin kayayyaki da karuwar rashin aikin yi da faduwar darajar hannayen jari a Amurka, a lokacin da ta kaddamar da yakin haraji, wanda ya nuna cewa, maimakon cimma abun da take fata na samun fifiko, asara aka samu da lalacewar muradun kamfanoni da ’yan kasuwar kasar.

Kowace kasa tana da cikakken iko da ’yancin zabar manufofi da matakan da ya dace da ita. Da Sin ta tsaya kai da fata cewa ba za ta ba da kai a yakin haraji da Amurka ta tayar ba, hakan ya sa Amurka yin karatun ta nutsu, kuma ta tuntubi bangaren Sin domin tattaunawa.

Wadannan misalai sun nuna mana cewa, akwai hanyoyi masu sauki da inganci na samun maslaha, kuma shawarwarin da Sin take gabatarwa, su ne suka dace da yanayin duniya a yanzu. Ba dole sai kowa ya samu abun da yake so ba, amma hawa teburin sulhu da tuntubar juna tana taka muhimmiyar rawa wajen warware sabani, da lalubo inda kowane bangare zai iya saki, domin a samu mafitar da za ta karbu ga kowa. Kuma irin wannan din, shi ne burin sabuwar Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya da shugaban kasar Sin ya gabatar a baya bayan nan. Duniya ba ta bukatar mayar da hannu agogo baya ta hanyar tayar da rikice-rikice da danniya da nuna fin karfi, zamani ya sauya kuma dole salon tafiyar da harkoki ya sauya, domin dacewa da yanayin da ake ciki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Gombe ta gyara hanyoyin kiwo domin daƙile rikicin manoma da makiyaya
  • SEMA Jigawa Da NEMA Da UNICEF Sun Bada Horo Akan Agajin Gaggawa A Auyo
  • Gwamnatin Kano Ta Aika Dalibai 588 Zuwa Jihohin Arewa 13 A Karkashin Shirin Musanya
  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani