HausaTv:
2025-07-05@23:44:17 GMT

Falasdinawa 94 sun yi shahada a Hare-haren Isra’ila a rana guda

Published: 21st, May 2025 GMT

Bayanai daga Zirin Gaza ne cewa mutane 94 ne sukayi shahada a bayan hare-haren sakamakon harin wuce gona da iri da Isra’ila ta kai a zirin a cikin kwana guda.

Adadin ya karu sosai a baya ga kusan mutane 60 da kafafen yada labarai na Falasdinu suka sanar.

Isra’ila ta kai hare-haren ne kan gidaje, makarantu, da matsugunai da dai sauransu.

Alkalumman shahidai sakamakon hare-haren na Isra’ila tun soma yakin a watan Oktoban 2023 ya kai akalla 53,573, akasari mata da kananan yara.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Lukurawa Sun Kashe Mutane 15 a Sakkwato

Wasu ‘yan bindigar da ake zargi Lukurawa ne a wani sabon hari sun kashe mutane sama da 15 a Qaramar Hukumar Tangaza ta jihar Sakkwato, ranar Litinin da ta gabata.

Babban Jami’i a Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Qasa(Red Cross) reshen Sakkwato Alhaji Abubakar Ainu ya tabbatar wa Aminiya harin wanda ya yi matuqar tayar da hankalin mutanen yankin ganin an xauki dogon lokaci kafin kawo irin wannan hari mai muni.

Ainu ya ce, “jami’anmu na sa kai sun ziyarci qauyen Kwalajiya na mazabar Magoho a garin Tangaza domin jajantawa da kuma halartar sallah janaza ta muanen da ‘yan bindigar suka kashe sama da 15.  Waxanda suka jikkata an kai su Asibitin Kashi na Wamakko da Asibitin Koyarwa ta Xanfodiyo da na Qwararru a birnin jiha domin karvar magani.”

Ya ce yankin na cikin wuraren da ke fama da matsalar tsaro ta varayin shanu da masu tayar da qayar baya.

“Wannan lamari baya da daxi ko kaxan, dubi yadda aka mayar da wasu mata zawarawa aka mayar da wasu yara marayu domin biyan wata buqata wadda addini bai yarda da ita ba, ina kira ga hukuma ta sake salon yaqar ‘yan bindiga da take yi,” in ji Ainu.

Wani mazauni qauyen Kwalajiya ya ce ‘yan bindigar Lukurawa sun zo a qauyen a daren Lahadi har zuwa Asuba ta ranar Litinin in da suka kashe wasu mutane a harin da suka kai, a lokacin da suka yi ta harbi kan mai uwa da wabi.

“Bayan sun kashe mana mutane sun tafi da dabbobi masu yawa, duk da mutanenmu sun yi qoqari amma yawan mutane da makaman da suke xauke da su ya sa suka fi qarfinmu. Har zuwa yanzu ba mu san adadin waxanda aka kai asibiti ba domin suna da yawa, sai dai waxanda suka rasu 15 muka yi wa Sallah.

“Muna kira ga jami’an tsaro su mayar da hankali wurin korar mana waxannan ‘yan bindigar don mu samu zaman lafiya a jiha baki xaya.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lebanon: Mutum Daya Ya Yi Shahadi A Wani Hari Na HKI
  • Jaridar Telegraph: Makaman Iran Masu Linzami Sun Sauka Kai Tsaye Akan  Cibiyoyin Sojan Isra’ila Guda 5  
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kashe Masu Neman Karbar Kayan Agaji A Gaza
  • Aragchi Ya Musanta Zargin Da Jamus Take Watsawa Dangane sa Shirin Nukliyar Kasar
  •   Gaza: Fiye Da Falasdinawa 17 Ne Su Ka Yi Shahada Ayau Juma’a
  • Majalisar Mali ta ƙara wa Goita wa’adin mulkin shekara biyar
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Sake Aiwatar Da Kisan Kare Dangi Kan ‘Yan Gudun Hijiran Falasdinawa
  • Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal
  • Lukurawa Sun Kashe Mutane 15 a Sakkwato
  • Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram