Kotu Ta Daure Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Mutum A Gidan Yarin Adamawa
Published: 19th, May 2025 GMT
Wadanda ake tuhumar dai, a cewar rahoton farko, sun yi wa mamacin dukan tsiya har sai da ya suma, inda aka garzaya da shi Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya ta Hong inda wani likita ya tabbatar da mutuwarsa.
Dukkan wadanda ake tuhumar dai sun ki amsa laifin da ake zarginsu da aikatawa lokacin da aka karanta musu tuhume-tuhumen.
Kotun da ke karkashin Alkali Uwani Danladi, ta bayar da umarnin a garkame wadanda ake kara a gidan gyaran hali don bai wa ‘yansanda damar kammala bincike tun da har yanzu akwai sauran mutum daya da ake tuhuma.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Togo: An Kashe Mutane 7 A Zanga-zangar Kin Jinin Gwamnati
Masu fafutuka a kasar Togo sun sanar da cewa an kashe mutane 7 a yayin Zanga-zangar nuna kin jinin gwamnati da aka yi a makon da ya shude, suna masu tuhumar jami’an tsaro da yin amfani da karfin da ya wuce haddi.
Kamfanin dillancin labarun “Reuters” wanda ya nakalto ‘yan fafutukar na kasar Togo, suna cewa; Jami’an tsaro sun yi amfani da karfi mai ban tsoro akan masu Zanga-zangar.”
Kungiyoyin fararen hula da na masu kare hakkokin dan’adam 12 ne su ka fitar da sanarwar, su ka kuma kara da cewa; jami’an tsaron kasar sun yi amfani da kulake wajen dukan masu Zanga-zangar, haka nan kuma igiyoyi da suke daure su, kamar kuma yadda su ka sace da lalata dukiyar mutane.
Har ila yau kungiyoyin sun sanar da samun gawawwakin mutane 3 a ranar juma’ar da ta gabata, 2 daga cikinsu na kananan yara ne da aka jefa a cikin wani tafki a gabashin birnin Lome. Sai kuma gawawwaki 2 na wasu ‘yan’uwa a tafkin yankin Icodesio, shi ma a cikin birnin Lome. Sai a ranar Asabar ne aka sami cikon gawawwakin mutane 2 a yankin Niconakiboyi.
Bayanin da ya fito daga gwamnatin kasar a ranar Lahadi shi ne cewa, mutanen da aka samo gawawwakinsu sun nitse ne a cikin ruwa, tare da taya iyalan wadanda su ka rasa rayukan nasu alhinin rashin da su ka yi.
Masu Zanga-zangar dai suna nuna kin amincewa da yin dandazon mukamkan gwamanti a hannun shugana kasar da kuma rashin Shata hanyar kawo karshen abinda suke ganin a matsayin kama-karya.
Kungiyar kare hakkin bil’adama ta “Amnesty International” ta bayyana abinda yake faruwa da ‘murkushe ‘yan hamayya.