‘Yansanda Sun Daƙile Yunƙurin Yin Garkuwa Da Mutane A Katsina
Published: 5th, May 2025 GMT
“A ranar 2 ga Mayu, 2025, wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne dauke da makamai sun kai hari kan wani Abu Iro, wani matashi dan shekara 23 a karamar hukumar Faskari, inda suka Sara masa Adda a kokarinsu na tafiya da shi.
“Bayan samun rahoton, cikin gaggawa tawagar jami’an ‘yansanda tare da kungiyar tsaro ta cikin al’umma ta jihar Katsina (KSCWC), karkashin jagorancin babban jami’in tsaro na Faskari, suka amsa kira, inda suka dakile yunkurin yin garkuwa da mutane, tare da samun nasarar kubutar da wanda aka sace.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
IRGC: Duk Wani Wuce Gona Da Iri Na ‘Yan Sahayoniya Zai Gaggauta Rushewarsu
Dakarun kare juyin musulunci na Iran sun fitar da bayani a lokacin tunawa da sace jami;an diplomasiyyar Iran 4 a birnin Beirut, wanda ya kunshi cewa: Ya zama wajibi ‘yan sahayoniya su kwana da sanin cewa; Duk laifukan da su ka aikata a baya za a yi musu sakamako a kansa,kuma duk wani sabon wuce gona da iri, zai gaggauta zuwa karshensu ne.”
Sanarwar ta kuma ce: Muna tunawa ne da zagayowar cikar shekaru 42 daga wancan aikin ta’addanci, da a yanzu kwanaki kadan ne su ka wuce na kawo karshen yakin da HKI da Amurka su ka kallafa mana na tsawon kwanaki 12. Yaki ne wanda martani mai karfi da jamhuriyar musulunci ta Iran ta mayar yake kara fito da raunin da wannan kirkirarriyar kasa take da shi.
Har ila yau bayanin na dakarun kare juyin musulunci na Iran ya bayyana yadda jamhuriyar musulunci ta Iran ta yi ta kokari a fagen diplomasiyya akan batun jami’an diplomasiyyar da Isra’ila ce ta sace su ta hanyar ‘yan korenta,kuma hatta babban magatakardar MDD a 2008 ya bayyana cewa a shirye yake ya bayar da hadin kai domin ganin an warware batun,amma kuma abin takaici har zuwa yanzu wadanda su ka aikata laifin ba su fuskanci sakamakon da ya dace da su ba.
A dalilin haka dakarun kare juyin musuluncin suke kara tunatar da MDD da kuma kungiyar agaji da “Red Cross” da su yi aiki da nauyin da ya rataya a wuyansu akan wannan batun. jami’an diplomasiyyar da HKI ta yi garkuwa da su sun hada janar Alhaj Ahmad Mutawassiliyan, sai Sayyid Muhsin Musawi, Taki Rastigar Mukaddam, da kuma Kazim Akawan.