Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-05-02@22:37:53 GMT

Amurka Ta Cire Haraji Kan Kaya Marasa Tsada Daga China

Published: 2nd, May 2025 GMT

Amurka Ta Cire Haraji Kan Kaya Marasa Tsada Daga China

Amurka ta kawo ƙarshen cire haraji kan wasu kayayyaki da ba ma su tsada ba da ake shiga da su ƙasar daga China.

 

A baya Amurkawa na iya sayan kayayyakin China da ba su haura dala 800 ba, idan za su yi oda ta intanet ba tare da wani haraji ba, amma yanzu za su biya kashi 120.

 

Ana sa ran harajin zai fara aiki nan take, kuma wasu Amurkawa masu sayayya za su ji a jikinsu.

 

Hakazalika su ma yawancin kamfanonin China da ke samar da kayan da shigar da su can.

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Amura

এছাড়াও পড়ুন:

Dubban Mutanen Burkina Faso Sun Yi  Gangamin Nuna Goyon Bayan Shugaban Kasa Ibrahim Traore

Kwanaki kadan bayan  wani furuci daga babban jami’in sojan Amurka a Afirka akan shugaban kasar ta Burkina, dubban mutanen kasar sun  yi gangami na nuna goyon bayan Kaftin Ibrahim Traore

Gangamin na mutanen kasar Burkina Faso, ya biyo bayan maganganun da su ka fito daga kwamandan sojojin Amurka a Afirka Janar Michael Langley wanda ya zargi sojojin dake Mulki da amfani da ma’adanan kasar saboda kashin kansu maimakon yi wa mutane aiki.

Mahalarta gangamin sun daga kwalaye dake dauke da rubutun yin tir da furucin jami’in sojan na Amurka da kuma nuna goyon baya ga shugaban kasar.

 Daga cikin mahalarta gangamin da akwai fitaccen mawakin kasar, Ocibi Joan,wanda ya siffata jami’in sojan Amurkan da dabbar daji mai cin mutane yana mai yin kira a gare shi da kasarsa da su daina yin karya.

Haka nan kuma ya kara da cewa: ” Mutanen Burkina ba su fada da kowa,amma a lokaci daya, ba za su bar masu wawason dukiyar kasarsu ba.”

Wani mutum da ya halarci gangamin Haruna Sawadogo ya fada wa manema labaru cewa, idan suna son ganin bayan Kaftin Traore ne, to su fara ta kan mutanen kasar.

Hakan nan kuma jaddada cewa ba za su bari abinda ya faru da Thoms Sankara ya faru dakanar Troare ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Na Tantance Sakonnin Amurka Na Neman Tattaunawa A Kan Karin Haraji 
  • FIRS Ta Umarci Bankuna Su Rufe Asusun Ajiyar Tara Harajin Da Ba Su Cika Ka’ida Ba
  • Amurka ta sake kai Hari a yankunan Saada da Hudaidah na Yemen
  • Dubban Mutanen Burkina Faso Sun Yi  Gangamin Nuna Goyon Bayan Shugaban Kasa Ibrahim Traore
  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • Binciken Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Cin Zali Ta Hanyar Kakaba Haraji Ya Illata Kimar Amurka
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
  • Yadda ta kaya a wasannin kusa da na ƙarshe na Gasar Zakarun Turai