Aminiya:
2025-08-01@01:18:59 GMT

Hisbah ta kama tsohuwa kan zargin lalata da almajiri a Bauchi

Published: 21st, April 2025 GMT

Hukumar Hisbah ta kama wata mata mai sana’ar ɗan wake kan zargin ta da yin lalata da wani almajiri dan shekara 14 a garin Azare da ke Jihar Bauchi.

Shugaban Hukumar ta Hisbah na shiyyar Katagum da ke Azare, Malam Ridwan Muhammad  Khairan ya bayyana cewar, ana zargin matar, wadda ake kira Baba Mai Ɗan Wake da laifin yin fasikanci ta hanyar tilasawa da yaudara da wani almajiri dan kimanin shekaru 14, bayan ta sanya masa maganin ƙarfin maza a cikin lemon kwalba don ya riƙa biya mata buƙata.

Ya ce almajirin ya haɗu da Nana Mai Ɗan Wake da yake mata wanke-wanke a Sabuwar Tashar Jama’are ne, a cikin garin Azare, inda ta buƙaci ya riƙa zuwa gidanta yana kwana, inda ta rika yaudarar sa har ta riƙa yin lalata da shi.

A cewar Malam Ridwan Mohammed Khairan, sun cafke matar ne bayan samun labari cin zarafin almajirin ta hanyar neman sa da ya riƙa biya mata buƙata irin ta mata da miji. Ya ce almajirin da kansa ya gudu ya nemi mai unguwa domin a kuɓutar da shi daga wannan hali da ta sanya shi ciki.

Don haka suka kai rahoton ga Hukumar Tsaron Farin Kaya Sibli Difens (NSCDC) aka kamo ta aka yi mata binciken kwakwaf, daga nan aka kai ta Bauchi ofishin masu binciken manyan laifika (CID) don kammala binciken kafin a mika ta ga kotu.

Wata majiya ta ce wajen da matar take sana’ar dan waken ya zama babban dandalin ɓarayi da ’yan shaye-shaye da ƙananan mata masu zaman kansu, domin duk wadda aka kama a samame, takan ce a wajen baba mai ɗan wake take.

Da aka tambayi almajirin abin da ke faruwa tsakaninsa da ita? Ya ce da farko bara yake zuwa, sai ta ce, ya rika zuwa gidanta tana ba shi abinci.

Ya ce da yake zuwa gidanta bayan ta tashi a kasuwancinta, sai ta riƙa kai shi ɗakinta tana ba shi abinci da lemon kwalbar da take sa maganin a ciki, tare da umartar sa ya riƙa matsa mata jikinta daga nan sai ta rika jan sa kanta tana kama gabansa tana sawa a cikin nata.

Yaron ya ce haka suka rika yi tun kafin azumi har bayan azumi, alhali shi ba abin da yake ji sai ciwon baya da yake addabar sa, wanda hakan ta sa ya gudu ya yi ƙara wajen mai unguwa.

Yanzu dai Shugaban Ƙungiyar Alarammomi na Ƙasar Katagum, Alaramma Husaini Gwani Gambo da Ƙungiyar Mata Musulmi ta FOMWAN da Ƙungiyar Matasa Masu Neman Hakkin Dan Adam, sun sa hannu don ganin an yi hukunci a kanta da bukatar tashinta a garin Azare.

Shugaban ƙungiyar alarammomin ya tabbatar da cewar, za su yi duk yadda za su yi don ganin an bi musu hakkin wannan cin zarafin da aka yiwa almajirinsu ba don ganin ya zama darasi ga wasu irin ta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bana mai ɗan wake

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya tsawaita wa’adin aikin shugaban hukumar Kwastam

Shugaba Bola Tinubu ya ƙara wa Bashir Adeniyi, Shugaban Hukumar Kwastam ta Ƙasa, karin shekara ɗaya a kan wa’adin da ya kamata ya yi na shugabancin hukumar.

Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa a ranar Alhamis.

Mutum 9 sun rasu a hatsarin kwale-kwale a Jigawa NNPCL ya sake haƙa sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani

A cewarsa, wa’adin Mista Adeniyi zai ƙare ne a ranar 31 ga watan Agusta, 2025.

Amma yanzu Shugaba Tinubu ya amince da ƙara masa shekara ɗaya, wanda hakan ke nufin zai ci gaba da zama a kan kujerarsa har zuwa watan Agustan 2026.

Sanarwar ta bayyana cewa ƙarin wa’adin zai ba shi damar kammala wasu muhimman ayyuka da yake yi.

Waɗannan ayyukan sun haɗa da gyara da inganta harkokin Kwastam, kammala wani shiri da zai sauƙaƙa kasuwanci a Najeriya, da kuma taimaka wa ƙasar wajen cika alƙawuran da ta ɗauka ƙarƙashin yarjejeniyar ciniki ta Afirka (AfCFTA).

Shugaba Tinubu, ya yaba da ƙwazon Mista Adeniyi da yadda yake gudanar da ayyukansa.

Ya ce ƙarin wannan wa’adin zai taimaka wajen inganta hanyoyin tara kuɗaɗen shiga a hukumar, da kuma tabbatar da tsaro a iyakokin Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Horas Da Mata 600 Kan Abincin Yara Mai Gina Jiki A Jigawa
  • Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika
  • Tinubu ya tsawaita wa’adin aikin shugaban hukumar Kwastam
  • Tinubu ya tsawaita wa’adin shugaban hukumar Kwastam
  • Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC
  • Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki
  • Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri
  • EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Akwa Ibom