Mutane da dama ne suka mutu sannan wasu sun jikkata sakamakon wasu sabbin hare-hare da jiragen yakin Amurka suka kai kan wasu yankuna na kasar Yemen.

A daren jiya wayewar yau Lahadi, sojojin Amurka sun kai hare-hare ta sama akalla 20 a Sanaa babban birnin kasar Yemen, da kuma yammacinta da gabashi da kuma kudancin kasar.

Hare-haren na zuwa ne a daidai lokacin da mahukuntan kasar Yemen suka sanar a ranar Asabar cewa kimanin mutane 80 ne suka mutu, yayin da wasu 150 suka samu raunuka sakamakon harin da Amurka ta kai a ranar Juma’a a tashar mai na Ras Issa da ke birnin Hudaidah.

Hare-haren na Amurka a Yemen sun kara gurgunta halin da kasar ta Yemen ke ciki.

Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya bayyana matukar damuwarsa game da abubuwan da suka faru a baya-bayan nan, ciki har da hare-haren da aka kai a kusa da tashar ruwan Ras Issa.

Kakakin Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Stéphane Dujarric, ya bayyana a wata sanarwa jiya Asabar cewa, “Guterres ya damu matuka da hare-haren da Amurka ta kai a ranakun 17 da 18 ga watan Afrilu a ciki da wajen tashar jiragen ruwa na Ras Issa na kasar Yemen, wanda ya yi sanadin jikkatar fararen hula da dama, ciki har da ma’aikatan agaji biyar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Yemen

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila

Dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC) sun kaddamar da wani sabon harin makamai masu linzami da jirage marasa matuka kan Isra’ila a cikin daren jiya Asabar, biyo bayan matakin farko na harin ramuwar gayya na kan harin Isra’ila na ranar Juma’a.

Jim kadan bayan harba makamai masu linzami da jirage marasa matuka, sashen hulda da jama’a na IRGC ya ba da sanarwar kaddamar da wani sabon shiri na manyan makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka.

Sanarwar ta yi nuni da cewa, sashen kula da sararin samaniya na IRGC ya fara wannan sabon mataki na aikin a matsayin mayar da martani kai tsaye ga sabbin ta’addancin gwamnatin sahyoniyawan.

Babban abin da aka fi mayar da hankali kan wannan sabon farmakin na ‘Operation True Promise III’ an bayar da rahoton cewa, birnin Haifa mai tashar jiragen ruwa ya kunshi muhimman wuraren soji da masana’antu na gwamnatin.

Hare-haren sun shafi wasu muhimman cibiyoyin soji da masana’antu na Isra’ila, da suka hada da matatun mai da na wutar lantarki a Haifa, inda aka ce gobara ta tashi a sanadiyar haka.

Daya daga cikin faifan bidiyon ya nuna wata gagarumar gobara da ta tashi a matatar mai ta Haifa bisa tasirin da manyan makamai masu linzami na Iran suka yi, wanda ya haskaka sararin samaniyar yankunan da aka mamaye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta kai sabbin hare-hare birnin Tel Aviv da Haifa
  • Iran Ta Cilla Makamai Kan HKI Da Rana A Karon Farko A Yau Lahadi
  • Sojojin Kasar Iran Sun Ce Bazasu Dakatar Da Yaki ba Har Zuwa Samun Nasara A kan HKI
  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila
  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Iran, ta yi wa Isra’ila ruwan makamai masu linzami
  • Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu