Wasu mutane sun yi shahida tare da jikkata sakamakon hare-haren wuce gona da iri da Amurka ta kai kan kasar Yemen

Ma’aikatar lafiya ta kasar Yemen ta sanar a yammacin jiya Asabar cewa: An kashe mutane uku tare da jikkata wasu da dama a hare-haren da jiragen yakin kawancen da Amurka ke jagoranta suka kai a biranen Sana’a, Amran da Ma’arib.

Ma’aikatar ta lafiya ta kara da cewa: ‘Yan kasar Yemen 7 ne suka jikkata sakamakon harin wuce gona da irin da Amurka ta kai kan unguwar Al-Nahda da ke gundumar Al-Thawra, sannan wani dan kasar ya jikkata a gundumar Al-Safiyah sakamakon wani hari da aka kai a makabartar Majel Al-Dama da ke babban birnin kasar, kuma ta yi nuni da cewa “dan kasa daya ya yi shahada yayin da wani kuma ya samu rauni sakamakon harin wuce gona da iri da gwamnatin Amurka ta kai a gundumar Matar’a a gundumar Safiya.”

A yammacin ranar Asabar ne dai dakarun Amurka suka kaddamar da wasu hare-hare ta sama a babban birnin kasar Sana’a fadar mulkin kasar. Sannan jiragen saman Amurka sun kai hari kan unguwar Al-Nahda da ke gundumar Al-Thawra tare da kai wasu hare-hare kan wasu yankuna.

Hakazalika, sojojin Amurka sun kai hari kan makabartar Majil Ad-Dama da ke gundumar As-Safiyah, lamarin da ya yi sanadin jikkata wani dan kasar Yemen. Hakazalika jiragen makiya sun kai hare-hare 4 a yankin Al-Hafa, hari guda daya a kan makabartar Al-Najimat da ke gundumar As-Sab’een, da hari guda 5 da suka kai kan filin shakatawa na 21 ga Satumba a gundumar Ath-Thawra.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: da ke gundumar kasar Yemen

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Sanar Da Dakatar Da Tattaunawa Da Amurka A Wannan Lokaci Da Take Fuskantar Yaki Daga Isra’ila
  • Kungiyar Abokan Yarjejeniyar M.D.D Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ke Kai Wa Kan Iran
  • Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila
  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bude Kofofin Jahannama Ga Yahudawan Sahayoniyya
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba