Wasu mutane sun yi shahida tare da jikkata sakamakon hare-haren wuce gona da iri da Amurka ta kai kan kasar Yemen

Ma’aikatar lafiya ta kasar Yemen ta sanar a yammacin jiya Asabar cewa: An kashe mutane uku tare da jikkata wasu da dama a hare-haren da jiragen yakin kawancen da Amurka ke jagoranta suka kai a biranen Sana’a, Amran da Ma’arib.

Ma’aikatar ta lafiya ta kara da cewa: ‘Yan kasar Yemen 7 ne suka jikkata sakamakon harin wuce gona da irin da Amurka ta kai kan unguwar Al-Nahda da ke gundumar Al-Thawra, sannan wani dan kasar ya jikkata a gundumar Al-Safiyah sakamakon wani hari da aka kai a makabartar Majel Al-Dama da ke babban birnin kasar, kuma ta yi nuni da cewa “dan kasa daya ya yi shahada yayin da wani kuma ya samu rauni sakamakon harin wuce gona da iri da gwamnatin Amurka ta kai a gundumar Matar’a a gundumar Safiya.”

A yammacin ranar Asabar ne dai dakarun Amurka suka kaddamar da wasu hare-hare ta sama a babban birnin kasar Sana’a fadar mulkin kasar. Sannan jiragen saman Amurka sun kai hari kan unguwar Al-Nahda da ke gundumar Al-Thawra tare da kai wasu hare-hare kan wasu yankuna.

Hakazalika, sojojin Amurka sun kai hari kan makabartar Majil Ad-Dama da ke gundumar As-Safiyah, lamarin da ya yi sanadin jikkata wani dan kasar Yemen. Hakazalika jiragen makiya sun kai hare-hare 4 a yankin Al-Hafa, hari guda daya a kan makabartar Al-Najimat da ke gundumar As-Sab’een, da hari guda 5 da suka kai kan filin shakatawa na 21 ga Satumba a gundumar Ath-Thawra.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: da ke gundumar kasar Yemen

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar

Ma’aikatar leken asiri na JMI ta bada sanarwan cewa ta gano shirin makiya na kashe manya-manyan Jami’an gwamnati har 35 a kasar kafin yakin da suka dorawa kasar.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto majiyar ma’aikatar na fadar haka, ta kuma kara da cewa a cikin yakin kwanaki 12 sun yi kokarin kashe many-manyan Jami’an gwamnati har 35 a cikin yakin. Da kuma wasu 13 watanni kafin yakin, amma saboda matakan da ma’aikatar ta dauka hakan bai faru ba.

Labarin ya kara da cewa, hukumar a tsaye take kan makirce-makircen makiya, sannan kuma tana daukar matakan da suka dace don hana  kutsawar su a cikin kasar da kuma cutar da shuwagabanni da kuma mtanen gari.

A wani bangare kuma hukumar ta bayyana cewa tana ayyukan leken asiri kan HKI da kuma shirye-shiyenta nag aba. Tana samun ma’aikata a cikin sojoji da jami’an tsaro na HKI. Sannan ta kara da cewa ma’aikatansu kadanne yahudawan suka kama.

Majiyar ta kara da cewa ta sami bayanan sirri kan shirye-shrye masu muhimmanci na HKI daga ciki har da bayani dangane da shirinta na makaman Nukliya.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Najeriya: Likitoci a Lagas Sun Shiga Yajin Aiki July 29, 2025  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai July 29, 2025 Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu July 29, 2025  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta July 29, 2025 Manjo Janar Musawi: Ko Kadan Ba Mu Yarda Da Amurka Ba July 29, 2025 Araqchi: Iran Zata Mayar Da Martanin Da Ba Zai Yiwu A Boye Ba  Kan Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kanta July 29, 2025 Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza July 29, 2025 Rasha Ta Mayar Da Martani Ga Shugaban Amurka Kan Gindaya Wa’adin Kawo Karshen Yakin Ukraine July 29, 2025 Kasar Faransa Ta Yi Allah Wadai Da Harin Ta’addancin Da Aka Kai Birnin Zahedan Na Kasar Iran July 29, 2025 Wakilin Gidan Talabijin Na Al-Alam Ya Bayyana Yadda Shi Da Iyalansa Suka Rayu Kwanaki Biyu Babu Abinci A Gaza July 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Shugaban Kasar Lebanon Aun Ya Ce Mun Aike Wa  Amurka Sakwanni Akan Dakatar Da Hare-haren HKI
  • Hare-hare: ’Yan bindiga sun raba mutum 5,000 da muhallansu a Katsina
  • Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku  
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami
  • Mutum daya Yayi Shahada 4 Sun Ji Rauna Sanadiyar Hare-Haren HKI A Lebanon
  • Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar
  • Kasar Faransa Ta Yi Allah Wadai Da Harin Ta’addancin Da Aka Kai Birnin Zahedan Na Kasar Iran
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • Iran Ta Ce Amurka Ce Bayan Hare-haren Da Aka Kai Zahidan
  • Mutanen Sweida Na Kasar Siriya Suna Fama da Rashin Abinci da Ruwa