Wata Cibiyar Kare Hakkin Bil’Adama Ta Bukaci Kama Jami’in Haramtacciyar Kasar Isra’ila A Kasar Birtaniya
Published: 17th, April 2025 GMT
Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Hind Rajab ta yi kira ga Birtaniya da ta kama ministan harkokin wajen haramtacciyar kasar Isra’ila
Kungiyar kare hakkin bil’adama ta Hind Rajab ta gabatar da bukatar fitar da sammacin kame ministan harkokin wajen haramtacciyar kasar Isra’ila Gideon Sa’ar da yake ziyara a Birtaniya.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo cewa: Cibiyar Hind Rajab Foundation da ta mayar da hankali kan neman gurfanar da sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila da ake zargi da aikata laifukan yaki, ta mika bukatar kama Gideon Sa’ar a birnin Landan na Birtaniya.
Kafofin watsa labaran haramtacciyar kasar Isra’ila sun jiyo ofishin ministan harkokin wajen haramtacciyar kasar Isra’ila na cewa babu wata niyyar takaita ziyarar Sa’ar a Biritaniya ko kuma sauya jadawalinsa sakamakon wannan bukata.
A cikin wata sanarwa da cibiyar Hind Rajab ta fitar ta ce: Tana ci gaba da kokarin ganin an fitar da sammacin gaggawa kan kame Sa’ar, mamba a majalisar ministocin tsaron gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila.
Cibiyar ta yi ikirarin cewa: Gideon Sa’ar ya taimaka tare da karfafa aiwatar da laifuka da suka hada da keta dokokin jin kai na kasa da kasa a Falasdinu, ciki har da azabtarwa, kisa da gangan da kuma lalata dukiyoyi.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: haramtacciyar kasar Isra ila
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Da Masar Sun yi Kira Da Kawo Karshen Keta Hurmin Gaza da Labanon da Isra’ila ke yi
A wata tattaunawa ta wayar tarho da ta gudana tsakanin ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi da takwaransa na kasar masar Badr Abdelatty sun bayyana cewa isra’ila na ci gaba da kai hare-hare da keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta a Gaza da kuma kasar labanon,
Ci gaba da keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta mai mataki 20 kan gaza,wanda shugaban Amurka Donald Trump ya gabatar hujja ce da ta tabbata tun daga farko kamar yadda rahotanni da suka fito daga yankin gaza suka bayyana cewa akalla mutane 366 ne abin ya shafa daga lokacin da aka cimma yarjejeniyar zuwa yanzu.
A watan nuwamba shekara ta 2024 ne aka cimma yarjejeniyar dakatar da bude wuta tsakanin kungiyar hizbulla da HKI bayan hare haren da isra’ila ta kai , da yin kisan kare dangi kan alummar gaza a watan oktoban shekara ta 2023
An tilastawa Isra’ila kulla yajejeniyar ce bayan kashi da ta sha a hannu hizbullah inda ta yi mummuna asara a filin daga, ta kasa cimma burinta bayan kashe mutane fararen hula 400 a kasar labanon.
Haka zalika ministocin harkokin wajen kasashen biyu sun yi musayar ra’ayi game da dangantar dake tsakaninsu kuma sun amince a ci gaba da tattaunawa sosai kan yadda za su kara fadada dangantakar dake tsakani
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Qatar Tayi Gargardi Game Da Gakiyar Yarjejeniyar Gaza Matukar Isra’ila Bata Janye Ba December 6, 2025 Gwamnatin Najeriya Za ta Karbi Sabon Bashin Dala Miliyan 500 A Bankin Raya Kasashen Afrika December 6, 2025 Kungiyoyin Kare Hakkin Bil Adama Sun Yi Gargadi Game Da Yunkurin Isra’ila Na Kashe Barghusi December 6, 2025 Gasar FIFA: Iran Ta Fada Cikin Group Mai Sauki A Gasar Kwallon Kafa Ta FIFA 2026 December 6, 2025 Kasashen Musulmi 8 Sun Ki Amincewa Da Korar Falasdinawa Daga Gaza December 6, 2025 Sojojin Afganistan Da Pakistan Sun Yi Musayar Wuta A Tsakaninsu Duk Tare Da Tsagait Wuta December 6, 2025 Rasha Tace Ta Kakkabo Jiragen Drones Na Ukrai 116 A Daren Jiya December 6, 2025 ‘Yar Iran ta isa wasan karshe na gasar cin kofin duniya na wasan harbi a karo na 4 December 6, 2025 Iran da Rasha sun rattaba hannu kan yarjejeniyoyi 20 da kwangiloli 5 a fannin fasaha December 6, 2025 Putin Na Rasha Ya Ce; Kasarsa Da India Za Su Kara Girman Kasuwancinsu December 6, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci