NAJERIYA A YAU: Mene ne Tasirin Shirin NYSC Bayan Shekaru 50 Da Kafa Shi?
Published: 7th, April 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Shirin bautar ƙasa wanda aka kafa tun a shekarar 1973, an ƙirƙire shi da nufin haɗa kan matasa daga kowane lungu da saƙo na ƙasar nan, domin fahimtar juna da kawar da wariyar yanki da ƙabilanci.
Amma a yau, bayan shekaru fiye da arba’in da biyar da fara wannan shiri, jama’a da dama na tambaya —ko har yanzu shirin na da tasirin da aka kirkire shi domin shi?
Ko har yanzu bautar ƙasa NYSC na ci gaba da samar da haɗin kai da ake buƙata a Najeriya?
NAJERIYA A YAU: Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta DAGA LARABA: Dalilan Da ’Yan Arewa Ke Tafiya Kudu FarautaShirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan ko har yanzu kwalliya na biyan kudin sabulu kan kafa shirin bautar kasa?
Domin sauke shirin, latsa nan
.উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta fitar, ta yi tir da harin na Isra’ila akan Iran tare da bayyana cewa, ya haifar da rikici a tsakanin bangarorin biyu da kuma musayar harba makamai masu linzami.
Gwamnatin ta Najeriya ta nuna bakin cikinta akan abinda ya faru, tare da kuma da yin kiran a tsagaita wutar yaki da gaggawa, da kai zuciya nesa.
Har ila yau, sanarwar ma’aikatar harkokin wajen ta Nigeria wacce kakakinta Kimiebi Imomotimi Ebienfa ya rattabawa hannu a yau Asabar,14 ga watan Yuni 2025, ta jaddada cewa; yaki ba zai maye gurbin tattaunawa ba, kuma hanyar diplomasiyya ce za ta kai ga samar da zaman lafiya mai dorewa, girmama juna da aiki da dokokin kasa da kasa.,