Leadership News Hausa:
2025-09-17@21:52:25 GMT

Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah

Published: 29th, March 2025 GMT

Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah

Sunana Naja’atu Baffa Jihar kaduna:

Ni dai a gaskia ban son akwai wani anko da za ai wannan sallar ko babu ba. Ina son saka takalmi mai dan tudu ba sosai ba, sai mayafi blue black, sai atamfa ta riga (half bubu) da ‘skirt’, sai sarka da dankunne da Awarwaro ‘silver’. Ina sha’awar cin Snacks irinsu meatpie, samosa, doughnut da kuma cake, sai kuma Yoghurt mai inibi.

Ina son in ziyarci kanwar babata wacce take a cikin garin Adamawa.

Sunana Aminu Adamu Malam Maduri A Jihar Jigawa:

To batun shidimar sallah sai mu ce Alhamdullilah domin duk tanadin da mutum yayi sai ya kare, duba da yadda kayayyakin suturu ko tufafi suke tsada don haka sai mutum yayi amfani da abun da ya samu, domin gudanar da bikin sallar cikin kwanciyar hankali ya fi komai dadi. To magana ta gaskiya shadda ita ce kalar kayan da zai fi yawa domin ita shadda ba a daina yayinta kuma tana daga cikin kalar suturar da duk mai hali ko sukuni zai so ya dinka, amma wasu kuma za su dinka yaduka domin kowa da irin kalar suturar da ta fi burge shi. To ni dai nafi sha’awar farin kaya musamman yadda manyan kaya ma’ana riga, binjima da wando da kuma hula fara wannan sune kalar suturar dana fi so musamman lokacin zuwa idi. Batun babu zabi duk wanda na samu zan ci, amma nafi son biskin alkama da miyar yakuwa ko jar miya. To da farko dai Masallacin idi shi ne guri na farko, sannan kuma sai ziyarce-ziyarce gidajen ‘Yan’uwa da abokan arziki.

Sunana Zainab Zeey Ilyas Jihar kaduna:

An yi wa sallah tanadi da dama kamar kayan da za a sa, Lalle, kitso, da sauransu. Bana tunanin gaskiya akwai wani anko da aka fitar domin a halin yanzu ko wa abin da Allah ya hore mai zai saka. Ina son saka shadda mai ‘stones’, ina son cin funkaso, tuwon shinkafa da miyar Agushi wadda ta ji ganda, kaji da kayan ciki, sai lemon ginger, sai farfesun zallar naman zabi.

Sunana Anas Bin Malik Achilafia Yankwashi A Jihar Jigawa:

Ana yin tanadi wa bukukuwan Sallah da yawa, amma dai ni kam babu tanadin dana yi wa sallar bana, batun anko  ko yayin kayan da ake siya, ni dai kam har yau ban lura ba, amma dai bana Iyalai na suna sha’awar Shadda, kuma gaskiya ba na ina sha’awar cin sakwara da hadadden lemu (Ubangiji Allah ka kara hore mana). A bisa al’ada kuma muna kaiwa ‘yan’uwa da abokan arzuka ziyara, tare da taya murnar kammala ibada. Ubangiji Allah karva mana ibada, ya sa mun dace.

Sunana Muhammad Isah Zareku Miga A Jihar Jigawa:

Tanadin dana yi wa wannan sallah shi ne ina so ta same ni cikin koshin lafiya da kuma ‘yan canji a cikin aljihuna. Wannan shekarar ta zo da son yin wankan shadda wato shampoo ita ce kowacce saurayi ko budurwa take/yake son sakawa duk da tsadar rayuwa da muke fama da ita. Ina sha’awar saka farar sutura ko shadda da farar hula a lokacin tafiya sallar idi. Abincin da nake muradin ci sh ine funkaso da jar Miya da naman kaji. Ina son kai ziyara zuwa gidan ‘Yan’uwa da abokan arziki in sha Allah.

Sunana Lawan Isma’il (Lisary) Jihar kano Rano LGA:

Babban tanadi shi ne Allah ya nuna mana ita muna raye da koshin lafiya. Haka ne kam duk da ana cikin yanayi ba za a rasa wadanda suka yin ba amma mu masu iyali iya yaranmu da iyayensu muka samu muka yi wa. da son samune ni dai sabuwar shadda fara idan kuwa ba ita ba to na sami koda koriya ce ko yadi shi ma fari ko koren. Waina da kunun daka ko na alkama da miya. Bayan dawowa daga sallar idi zan je gidan mahaifina da kuma gidan surukaina sai kuma na ‘yan’uwa da abokaina na kusa domin kara sada zumunci. Allah ya karvi ibadunmu.

Sunana Aisha T. Bello Jihar kaduna:

Sallah bikin daya rana in ji masu magana, a gaskiya na yi ma wannan sallah tanadi babba in Allah ya sa muna da rabon gani. Zan sanyaya raina ta samar da abun da na fi so a ci da sha, zan kai ziyara, zan je kallon hawan sallah, sannan zan kikkira ‘yan’uwa domin taya su barka da sallah da yardar Allah. A gaskiya bana jin wannan sallar akwai wani tanadi na anko kamar kullum, duba da yanayin rayuwa ana ta abun ci da sha ne, ina sha’awar saka doguwar riga da salla in sha Allah, sannan in sa babban mayafi in halarci sallar idi. In Allah ya ba ni dama ina so in kai ziyara jihar katsina don ganin dangina da ‘yan’uwa in sha Allah.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Sallah Ƙarama Taskira ina sha awar Ina sha awar

এছাড়াও পড়ুন:

Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta

Shugaban Ƙaramar Hukumar Birnin Kano, Alhaji Salim Hashim Idris Gwangwazo, ya kaddamar da shirin kula da ido kyauta domin tallafawa jama’a da ke fama da ‘Glaucoma’ da ke lalata rijiyoyin ido, da ‘Cataract’ wato yanar ido da sauran cututtukan ido.

An gudanar da shirin ne a Asibitin Kwalli tare da haɗin gwiwar gwamnatin jihar, ƙarƙashin Gwamna Abba Kabir Yusuf, da Hukumar Lafiyar Farko ta Jiha, da ƙaramar hukumar da masu bada tallafi daga kasashen waje.

Shirin ya haɗa da gwaje-gwajen lafiyar ido, da bayar da magunguna da kuma rarraba tabarau kyauta, musamman ga marasa ƙarfi a cikin al’umma.

Shugaban ƙaramar hukumar, ta bakin Kwamishinan Lafiya Alhaji Mustapha Darma, ya bukaci jama’a da su ci gaba da tallafawa gwamnati wajen samar da ingantaccen kulawa.

A baya-bayan nan, gwamnatin jihar ta dauki nauyin kula da lafiyar ido ga mutum  sama da 500 daga Birnin Kano da sauran kananan hukumomi.

Shugaban kula da lafiya am matakin farko na ƙaramar hukumar, Alhaji Lawan Jafar, ya ce wadanda lalurar su ba ta tsananta ba za a ba su shawarwarin kula da lafiyar su, da magunguna, wa su ma har da tabarau, yayin da wadanda ta su ta  tsananta kuma za a musu tiyata.

Wasu daga cikin wadanda suka amfana sun nuna godiya tare da yi wa gwamnati addu’a don samun nasara.

Shugaban tawagar likitocin, Dr. Kamal Saleh, ya tabbatar da cewa shirin ya samu nasara sosai.

 

Daga Khadijah Aliyu 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Gwamnatin Kano Ta Inganta Cibiyoyin Horas Da Sana’o’i Domin Dakile Aikata Laifuka Tsakanin Matasa
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar