Leadership News Hausa:
2025-08-01@05:01:57 GMT

Dangote Zai Gina Sabuwar Masana’antar Siminti A Jihar Ogun

Published: 22nd, March 2025 GMT

Dangote Zai Gina Sabuwar Masana’antar Siminti A Jihar Ogun

A cewarsa, tun da farko mun kau da kai ga barin sanya hannun jari a shiyyar kasuwanci ta Olokola (OKFTZ), amma saboda manufofinku da kuma yanayin da masu zuba jari ke da shi, ina so in ce mun dawo kuma za mu yi aiki tare da gwamnatin jihar don komawa Olokola, kuma ana shirin gina tashar jiragen ruwa mafi girma a kasar.

Da yake karin haske kan ayyukan da kamfanin ke gudanarwa a Jihar, Dangote ya ce sabbin layukan biyu masu karfin metric tan miliyan 6.0 a kowace shekara na kamfanin siminti an gina su a Itori, yayin da kamfanin siminti na metric ton miliyan 12 a kowace shekara kuma yana nan a Ibeshe.

Bayan kammala aikin, Dangote ya ba da tabbacin cewa, jimillar kamfanonin siminti a jihar za su yi makotaka da metric ton miliyan 18 a duk shekara, wanda zai zama jiha ko yanki mafi girma da ke samar da siminti a Afirka.

“Tare da gudunmawar sauran masu samar da siminti a Jihar, Ogun ta kasance a gaban sauran kasashen Afirka a fannin samar da siminti,” in ji shi.

Dangote ya bayyana cewa kamfanin simintin Dangote ne kan gaba wajen samar da siminti a nahiyar Afirka mai karfin metric ton miliyan 52.0 a duk shekara a fadin nahiyar Afirka.

Ya kara da cewa kashi 70 cikin 100 na simintin ana samar da su ne a Nijeriya, inda kamfanin Obajana da ke Jihar Kogi ke samar da metric ton miliyan 16.25 a duk shekara, wanda shi ne mafi girma a Afirka.

Ya ce zuba jarin da ake yi wajen sarrafa kayayyakin ya sa al’ummar kasar nan ta dogara da kanta wajen samar da siminti, kamar yadda kasar nan ta dogara da kanta wajen samar da taki, inda ake samun rarar kayayyakin da ake samu a kasuwannin ketare, wanda hakan ya sa al’ummar kasar ke samun kudaden musanya da ake bukata.

Yayin da yake lura da cewa burin kamfanin shi ne Nijeriya ta dogara da kanta a duk abin da ake samarwa, Dangote ya bayyana cewa a halin yanzu kamfanin yana biyan bukatun cikin gida na ‘Premium Motor Spirit’ (PMS) daga matatar mai 650,000 a kowace rana a Ibeju-Lekki, da kuma tace man jiragen sama da ‘Likuefied Petroleum Gas’ (LPG).

Ya ce, Nijeriya na kokarin farfado da tattalin arziki; Don haka akwai bukatar kamfanoni masu zaman kansu su kara kaimi ga kokarin gwamnati, yana mai ba da tabbacin cewa kamfaninsa zai ci gaba da nuna imaninsa ga al’ummar kasar da jama’arta ta hanyar zuba jari da nufin kawo sauyi ga tattalin arzikin kasar.

Da yake mayar da martani, Gwamna Abiodun ya jaddada cewa da kafa kamfanin siminti na Itori, zai samar da metric ton miliyan shida na siminti a duk shekara, kuma kamfanin da ake da shi na Ibeshe, yana samar da metric ton miliyan 12, don haka samar da siminti a jihar zai kai metric ton miliyan 18 a duk shekara, wanda zai zama mafi girma a samar da siminti a Nijeriya da kuma yankin Sahara.

Gwamnan ya yaba wa kamfanin bisa yadda bai yi kasa a gwiwa ba wajen aiwatar da ayyukan da suka dace na hadin gwiwa a tsakanin al’umma, kamar yadda a halin yanzu yake aikin gina titin ‘Inter-Change-Papalato-Ilaro’, yana mai tabbatar da cewa gwamnatinsa a shirye take ta hada kai da kamfanin domin ci gaban jihar da kasa baki daya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

NNPCL ya sake haƙa sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani

Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) ya sanar da sake haka sabbin rijiyoyin man fetur guda hudu yankin Kolmani na jihar Bauchi, kamar yadda Darakta a kamfanin, Yusuf Usman ya tabbatar.

Daraktan ya kuma sake jaddada aniyar kamfanin ta ganin ya fara aikin hako danyen man fetur a Arewacin Najeriya.

Samar da makamashi mai tsafta na zamani shi ne fatanmu — Guterres Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura

Ya bayyana hakan ne ranar Laraba a Kaduna a rana ta biyu ta taron tattaunawa tsakanin gwamnati da jama’a da Gidauniyar Tunawa da Ahmadu Bello ta shirya.

Daraktan ya ce, “Ya zuwa yanzu, NNPCL ya tono sabbin rijiyoyin danyen man fetur guda hudu a yankin Kolmani na jihar Bauchi, kuma yan kan aikin tantance fasahar da ta fi dacewa a yi aiki da ita a mataki na gaba a aikin.

“A wani yunkurinmu kuma na taimaka wa shirin Shugaban Kas ana komawa amfani da ababen hawa masu amfani da makamashin iskar gas a maimakon man fetur, yanzu haka ana can ana aikin gina tashoshin canza motoci zuwa masu amfani da gas na CNG da LNG,” in ji shi.

Ya ce da zarar an kammala aikinsu, ana sa ran tashoshin za su taimaka wajen bunkasa samuwar gas din kuma cikin sauki a Arewacin Najeriya.

Yusuf ya kuma zayyana wasu muhimman ayyuka da nasarorin da kamfanin ya samu a Arewacin Najeriya da ma sauran sassan kasar a karkashin mulkin Shugaban Kasa Bola Tinubu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Horas Da Mata 600 Kan Abincin Yara Mai Gina Jiki A Jigawa
  • NNPCL ya sake haƙa sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • Kamfanin NNPCL ya sake haka sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • Samar da makamashi mai tsafta na zamani shi ne fatanmu — Guterres
  • Man Utd Na Tattaunawa Da Golan PSG, Chelsea Ta Nace Wa Garnacho
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa
  • Shugaban SUBEB Yayi Alkawarin Bayar Da Tallafin Ilimi A Jihar Nasarawa
  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar da Manufar Sauyin Yanayi
  • Za mu halasta kafa ƙasar Falasɗinu muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba — Birtaniya
  • Muddin Isra’ila ba ta cika wasu sharuɗa ba za mu amince da kafa ƙasar Falasɗinu — Birtaniya