HausaTv:
2025-06-15@22:34:42 GMT

Syria: Sojojin HKI Sun Kai Wa Yankin Tartus Hari

Published: 4th, March 2025 GMT

Kamfanin dillancin labarun “Sana” na kasar Syria ya ambaci cewa; jiragen yakin HKI sun kai hare-haren a wani wuri dake gefen garin Tartus, sai dai babu rahoto akan asarar rayuka har yanzu.

Kamfanin dillancin labarun “ Sana” ya ci gaba da cewa; Ma’aikatan agaji suna kokarin gano hakikanin inda aka kai wa harin.

Su kuwa sojojin  HKI sun  sanar da kai hari ne akan wani rumbun makamai dake yankin “Kardaha’.

Wannan ba shi ne karon farko da sojojin na HKI su ka kai hari a garin Tartus ba,  a ranar 16 ga watan Disamba ba sun kai wannan irin harin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci

Babban sakataren kungiyar Hizbullah ta Lebanon Sheikh Na’im Kassim ya yi Allawadai da harin da HKI ta kai wa Iran, wanda ya bayyana shi da cewa; Yana da hatsarin gaske, kuma ‘yan sahayoniyar sun yi hakan ne bisa cikakken goyon bayan Amurka.

Sheikh Na’im Kassim ya kuma bayyana cewa; Harin na ‘yan sahayoniya ba shi da wani dalili da ya wuce a rufe bakin gaskiya wanda yake taimakawa al’ummar Falasdinu a Gaza da ake yi wa kisan kiyashi, haka nan kuma taimakawa da goyon bayan gwgawarmayar Lebanon da dukkanin wannan yankin.

Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kuma kara da cewa; Wannan harin da wuce gona da irin za iyi tasiri mai girma a cikin wannan yankin, sannan ya kara da cewa: Wannan harin ba zai wuce ba tare da fuskantar martani daga jamhuriyar musulunci ta Iran.

Haka nan kuma Na’im Kassim ya kara da cewa; Isra’ilawa makiya tare da Amurka ba za su taba yin tasiri akan hanyar da Iran ta zabarwa kanta ba ta gwgawarmaya ko kuma rawar da take takawa a cikin wannan yankin.

Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya ce; Hizbullah da magoya bayanta, suna ci gaba da riko da tafarkin gwagwarmaya da kuma goyon bayan jamhuriyar musulunci ta Iran wajen kare hakkokinta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna
  • Sojojin Kasar Iran Sun Ce Bazasu Dakatar Da Yaki ba Har Zuwa Samun Nasara A kan HKI
  • Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
  • Za A Watsa Shirin “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” A Kafofin Watsa Shirye-shiryen Kasashen Tsakiyar Asiya Biyar
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci