OPEC Da Kawayenta Zasu Kara Yawan Man Da Suke Haka A Karon Farko Tun Shekara Ta 2022
Published: 4th, March 2025 GMT
A wani rahoto wanda ba’a tantance ba kungiyar kasashe masu arzikin man fetur da kawayenta a wajen kungiyar OPEC + za su kara yawan man fetur da suke haka da ganga 138,000 a cikin watan Afrilu mai zuwa.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto wasu majiyoyin kungiyar wadanda ba’a bayyana ba suna cewa kungiyar OPEC + bata kara yawan man da take haka ba na lokaci mai tsawo, amma a halin yanzu zata kara kamar yadda aka sanar.
Labarin ya kara da cewa kungiyar tana rage ganga miliyon 5.85 wanda kuma shi ne kashi 5.7% na yawan man da ake haka a duniya, wannan kuma ya yi dai dai da shawarar da OPEC + suka dauka tun shekara ta 2022.
Labarin ya kara da cewa kasashen kungiyar sun amince da haka daga ciki har da kasar Rasha kasar da ta fi ko wace kasa hakar mai a duniya.
Akwai jitajitan cewa Amurka zata kara takurawa Iran a cikin watanni masu zuwa, amma Iran ta ce hakan ba zai shafi ta ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki
Majiyar tsaron kasar ta Kamaru sanar da cewa, da dama daga cikin sojojin kasar sun rasa rayukansu sanadiyyar wani hari da kungiyar Bokoharam ta kai musu ta hanyar amfani da manyan bindigogi da kuma jirgin sama maras matuki akan iyaka da Najeriya.
Majiyar ta ce an kai harin ne a yankin Sagami dake kusa da tafkin Chadi a gundumar Logun mai iyaka da kasar Najeriya.
Ita dai kungiyar Bokoharam ta addabi kasashen Najeriya, Kamaru da kuma jamhuriyar Nijar. Yankun arewacin kasar ta Kamaru ya fara fuskantar kai hare-hare daga wannan kungiyar ne tun a 2014 wanda kuma har yanzu yana ci gaba da faruwa daga lokaci zuwa lokaci.