Bidiyon batsa: Kotu ta ɗaure ’yan Tiktok biyu a Kano
Published: 4th, March 2025 GMT
Bidiyon batsa ya ja wa wasu ’yan Tiktok biyu hukuncin ɗaurin shekara guda kowannensu a gidan yari bayan an gurfanar da su gaban kotu a Jihar Kano.
Kotun Majiatare da ke Norman’s Land a Ƙaramar Hukumar Fagge ta yanke wasu ’yan Tiktok din hukunci ne bayan samun su da laifin saɓa wa dokokin Musulunci da kuma tsarin zamantakewar al’ummar jihar.
’Yan TikTok ɗin da suka haɗa da Ahmad Isa da Maryam Musa waɗanda dukansu ’yan unguwar Ladanai ne da ke yankin Hotoro ne.
Sun gurfana a kotu ne bayan da Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano ta cika hannunta da su.
Jami’an tsaro sun hana jama’a kwasar mai bayan hatsarin tanka a Taraba Yadda Kano ta koma matattarar ’yan TikTok bayan Hisbah ta daina kamensu NAJERIYA A YAU: Abin Da Ya Sa Ba Mu Bayar da ‘Ramadan Basket’ BaLauyan Gwamantin Kano, Barista Garzali Maigari Bichi, ya karanta wa matasan takardar tuhumar da ake musu na haɗa baki tare da yaɗa bidiyon da bai dace ba a dandalin sada zumunta, kuma sun amsa laifin.
Daga nan alƙalin kotun, Mai Shari’a Hadiza Muhammad Hassan ta yanke wa kowannensu hukuncin zaman shekara guda a gidan yari.
Ta kuma ba su zaɓin biyan tarar Naira dubu ɗari kowannensu, tare da gargaɗin su da su zama mutanen kirki.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan TikTok
এছাড়াও পড়ুন:
Sudan Ta Zargi Janar Haftar Na Libiya Da Goyon Bayan ‘Yan Tawayen Kasarta Na Rapid Support Forces
Ma’aikatar Harkokin Wajen Sudan na zargin Janar Haftar na Libiya da goyon bayan hare-haren ‘yan tawayen kasarta
Sojojin Sudan da ma’aikatar harkokin wajen Sudan sun zargi Janar Khalifa Haftar mai ritaya da goyon bayan hare-haren da dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces suka kaddamar a kan iyakokin Sudan da Masar da Libya.
A cewar sanarwar da Rundunar Sojin Sudan ta fitar, Dakarun Kai Daukin Gaggawa na Rapid Support Forces da ke samun goyon bayan Bataliyar Salafiyya ta Haftar, sun kai hare-hare kan iyakokin Sudan da Masar da Libya, da nufin kwace wadannan yankuna masu matukar muhimmanci.
Sanarwar ta kara da cewa: Wannan shiga tsakani da dakarun Haftar suka yi kai tsaye ya zama “cin zarafi a fili” ga ‘yancin Sudan da al’ummarta, tare da nuna cewa harin wani bangare ne na makircin kasa da kasa da na yanki bisa cikakkiyar masaniya da fahimtar kasashen duniya.
Sojojin kasar ta Sudan sun jaddada aniyarsu ta tunkarar wannan ta’addanci, ba tare da la’akari da irin makircin da ake kullawa ba, gami da tabbatar da aniyarsu ta kare ‘yancin kan kasa tare da goyon bayan al’ummar Sudan.