Yadda ’yan bindiga suka sace ɗalibai 4 a Jami’ar Tarayya ta Dutsinma
Published: 3rd, March 2025 GMT
’Yan bindiga sun yi garkuwa da ɗalibai huɗu a Jami’ar Tarayya da ke Dutsinma a Jihar Katsina.
’Yan bindigar sun sace daliban ne a ɗakunan kwanansu da ke yankin Paris Quarters a garin na Dutsinma.
Maharan ɗauke da bindigogi ƙirar AK-47 sun kutsa yankin ne da misalin ƙarfe 4 an asubahin ranar Lahadi, suka yi awon gaba da ɗaliban.
Jami’an tsaro sun kai ɗauki bayan samun kiran gaggawa, amma kafin su isa wurin ’yan bindigar sun riga sun riga sun tsere da ɗaliban.
Dutsinma na daga cikin ƙananan hukumomin Jihar Kastina da suka fi dama da matsalar ’yan bindiga da ke satar dabbobi da garkuwa da mutane domin karɓar kuɗin fansa, duk kuwa da matakan da gwamnati da kuma hukumomin tsaro ke ɗauka.
Duk da cewa zuwa lokacin da muka samu wannan labari kakakin ’yan sandan jihar, DSP Abubakar Sadiq, ko gwamantin jihar ba su fitar da sanarwa ba, amma wasu majiyoyin tsaro sun ce jami’an tsaro sun fara farautar maharan da nufin kuɓutar da ɗaliban cikin aminci.
Ana yawan samun matsalar garkuwa da ɗalibai musamman ba manyan makarantu a sakamakon matsalar rashin tsaro.
A watan Afrilun 2021 an sace ɗalibai kimanin 20 da ma’aikata biyu a Jami’ar Greenfield da ke Jihar Kaduna.
Daga bayan aka tsinci gawar uku daga cikin ɗaliban kafin daga bisani bayan watanni aka sako ragowar 14 da ke hannun ’yan bindiga.
Kazalika an sace ɗalibai da dama a Jami’ar Tarayya ta Gusau, waɗanda sai bayan tsawon lokaci aka sako su.
A watan Mayun 2024 aka sace ɗalibai tara daga Jami’ar Tarayya ta Confluence da ke Jihar Kogi a cikin aji.
Ƙo a watan Fabrairun 2025 a sace da ɗaliban Jami’ar Joseph Sarwuan Tarka da ke Makurdi, Jihar Binuwai.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Jami ar Tarayya a Jami ar Tarayya sace ɗalibai da ɗaliban yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
Daga Usman Muhammad Zaria
Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.
Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.
Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.
Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.
Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen tsaro.
CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.