Aminiya:
2025-06-15@19:09:54 GMT

Yadda ’yan bindiga suka sace ɗalibai 4 a Jami’ar Tarayya ta Dutsinma

Published: 3rd, March 2025 GMT

’Yan bindiga sun yi garkuwa da ɗalibai huɗu a Jami’ar Tarayya da ke Dutsinma a Jihar Katsina.

’Yan bindigar sun sace daliban ne a ɗakunan kwanansu da ke yankin Paris Quarters a garin na Dutsinma.

Maharan ɗauke da bindigogi ƙirar AK-47 sun kutsa yankin ne da misalin ƙarfe 4 an asubahin ranar Lahadi, suka yi awon gaba da ɗaliban.

Jami’an tsaro sun kai ɗauki bayan samun kiran gaggawa, amma kafin su isa wurin ’yan bindigar sun riga sun riga sun tsere da ɗaliban.

Dutsinma na daga cikin ƙananan hukumomin Jihar Kastina da suka fi dama da matsalar ’yan bindiga da ke satar dabbobi da garkuwa da mutane domin karɓar kuɗin fansa, duk kuwa da matakan da gwamnati da kuma hukumomin tsaro ke ɗauka.

Duk da cewa zuwa lokacin da muka samu wannan labari kakakin ’yan sandan jihar, DSP Abubakar Sadiq, ko gwamantin jihar ba su fitar da sanarwa ba, amma wasu majiyoyin tsaro sun ce jami’an tsaro sun fara farautar maharan da nufin kuɓutar da ɗaliban cikin aminci.

Ana yawan samun matsalar garkuwa da ɗalibai musamman ba manyan makarantu a sakamakon matsalar rashin tsaro.

A watan Afrilun 2021 an sace ɗalibai kimanin 20 da ma’aikata biyu a Jami’ar Greenfield da ke Jihar Kaduna.

Daga bayan aka tsinci gawar uku daga cikin ɗaliban kafin daga bisani bayan watanni aka sako ragowar 14 da ke hannun ’yan bindiga.

Kazalika an sace ɗalibai da dama a Jami’ar Tarayya ta Gusau, waɗanda sai bayan tsawon lokaci aka sako su.

A watan Mayun 2024 aka sace ɗalibai tara daga Jami’ar Tarayya ta Confluence da ke Jihar Kogi a cikin aji.

Ƙo a watan Fabrairun 2025 a sace da ɗaliban Jami’ar Joseph Sarwuan Tarka da ke Makurdi, Jihar Binuwai.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Jami ar Tarayya a Jami ar Tarayya sace ɗalibai da ɗaliban yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano

Rahotanni sun bayyana cewa wasu masu ƙwacen waya sun kashe wani ma’aikacin Jami’ar Northwest da ke Kano, Buhari Imam, ta hanyar daba masa wuta.

Bayanai sun nuna cewa barayin sun ritsa shi ne a yankin unguwar Sheka da ke karamar hukumar Kumbotso, inda suka sossoke shi da wuka a ciki kuma suka kwace wayarsa, a ranar Laraba.

BBC ya ruwaito mutumin ya rasu bayan da aka garzaya da shi Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano, a ranar Juma’a.

Shugaban ƙungiyar ma’aikatan jami’ar (NASU), Kwamared Bashir Muhammad, wanda ya tabbatar da aukuwar lamarin ya yi kira ga gwamnatin Jihar Kano da sauran hukumomi da su ɗauki tsattsauran mataki a kan kisan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga
  • Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa
  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara