Miji ya kashe matarsa saboda abincin buɗa-baki a Bauchi
Published: 2nd, March 2025 GMT
’Yan sanda sun cafke wani magidanci mai shekaru 50, Alhaji Nuru Isah kan zargin lakaɗa wa matarsa dukan da ya yi ajalinta a dalilin abincin buɗa-baki.
Bayanai sun ce taƙaddamar wadda aka soma gudanar da bincike a kanta ta auku ne a ranar Asabar a yankin Fadaman Mada da ke Jihar Bauchi.
Burina in yi fice kamar mahaifiyata — Maryam ‘Yar Auta Abubuwan da ya kamata a sani game da azumin watan RamadanaKakakin rundunar, CSP Ahmed Mohammed Wakil ya ce, “saɓani ne ya kaure tsakanin wani mai suna Nuru Isah mai shekara 50 da matarsa ta biyu, Wasila Abdullahi kan tsarin abinci da kayan buɗa-baki na gidan.
’Yan sanda sun ce bincike farko na nuna cewa mijin ya yi amfani da bulala wajen bugun matar mai shekaru 24, “inda ta yanke jiki ta faɗi, da aka kai ta asibitin koyarwa na jami’ar Tafawa Ɓalewa ne likitoci suka tabbatar da rasuwarta.”
Sanarwar ta ƙara da cewa ’yan sanda sun kama mijin, sun ɗauko bulalar da aka yi amfani da ita, sannan kuma za a yi binciken ƙwaƙwaf a kan gawar.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, Auwal Musa Muhammad, ya bayyana cewa za a gudanar da bincike domin tabbatar da adalci a lamarin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Azumin Ramadan Jihar Bauchi
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Hukumar Zaɓe Ta Bauchi, Ahmad Makama, Ya Rasu
Ya ce biyayyarsa ga doka da oda ya sa ya samu girmamawa daga abokan aikinsa da jama’a gaba ɗaya.
Gwamnan ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalansa, ’yan uwansa, abokansa da ma al’ummar masarautar Hardawa da ta Misau.
Ya roƙi Allah Ya gafarta masa, Ya jikansa, ya kuma sanya shi a Aljanna.
LEADERSHIP Hausa ta gano cewa aikin ƙarshe da Makama ya jagoranta a matsayin shugaban BASIEC shi ne zaɓen cike gurbi na shugaban ƙaramar hukumar Shira da mataimakinsa, a ranar 24 ga watan Mayu, 2025.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp