Aminiya:
2025-09-17@23:28:12 GMT

Sanata Natasha na neman diyyar N100bn wurin Akpabio

Published: 26th, February 2025 GMT

Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya a Majalisar Dattawa, Natasha Akpoti-Uduaghan ta shigar da ƙara a kotu tana ƙalubalantar shugaban majalisar, Godswil Akpabio, kan zargin ɓata mata suna.

Natasha ta shigar da ƙarar ne gaban Babbar Kotun Tarayya a ranar Talata, tana mai ƙarar Akpabio da babban mai taimaka masa Mfon Patrick.

Mutum 10 sun mutu a hanyar Damaturu zuwa Maiduguri Babu hannun Naira Marley a mutuwar Mohbad — Kotu

Ta nemi Kotun Tarayyar da ta umarci waɗanda ake karar su biya ta diyyar naira biliyan 100 kan zargin ɓata mata suna, sannan a biya ta naira miliyan 300 a matsayin kuɗin shigar da ƙara.

Akpoti, wadda lauyanta Victor Giwa ya shigar da ƙarar a madadinta, ya yi ƙorafi kan kalaman da babban mai taimaka wa Shugaban Majalisar Dattawan ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Ta nemi kotun ta tilasta wa mutanen janye kalaman, sannan su nemi afuwarta a wani shafin jarida.

Ta ɗora zargin nata ne kan wani saƙo da ta ce Mista Patrick ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda ya soke ta cewa “ba ta san komai ba game da zaman majalisa…da kuma saka tufafi masu shara-shara.”

Barista Giwa ya yi zargin cewar kalaman ba komai ba ne illa, ɓata suna, da takalar faɗa, da ƙanskantar da ita a idon abokan aikinta, da sauran al’umma.

Sanata Natasha ta buƙaci kotun da ta haramta wa waɗanda ake ƙara ko makusantansa daga wallafa duk wani rubutu na ɓatanci a game da ita.

A makon da ya gabata ne Sanata Natasha Akpoti Uduaghan ta bayyana damuwa kan yadda aka bai wa wani ɗan majalisa wurin zamanta, saboda wasu sauye-sauye da aka yi a tsarin zaman majalisar.

Sanatar ta ƙi amincewa da sauyin wajen zaman da aka yi mata, wanda hakan ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin ta da Akpabio.

Lamarin na zuwa ne yayin da aka umarci kwamitin ladabtarwa na Majalisar Dattawan da ya gayyaci Sanata Natasha don bin bahasi kan rikicin sauyin wajen zaman.

A bayan nan ne aka yi zazzafar musayar yawu tsakanin Sanata Natasha da Akpabio kan sauya mata wurin zaman da ta ce an yi ba tare da amincewarta ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: diyya

এছাড়াও পড়ুন:

DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu

Hukumar Tsaron Farin Kaya a Nijeriya DSS, ta gurfanar da fitaccen ɗan gwagwarmayar nan, Omoyele Sowore a kotu.

A ƙunshin ƙarar da DSS ta gabatar a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta haɗa da shafukan sada zumunta na X da kuma Facebook, inda take zarginsu da ba da ƙofar aibata Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Bida Poly ta sa sojoji kula da jarrabawar ɗalibai Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku

Darekan shigar da ƙara na Ma’aikatar Shari’a ta Tarayya, M.B Abubakar da wasu lauyoyi huɗu —M.E. Ernest da U.B. Bulla da C.S. Eze da kuma E.G. Orubor, ne suka shigar da ƙarar a madadin Gwamnatin Tarayya da kuma hukumar ta DSS.

DSS wadda ta kafa hujja da sashe na 24 da ke cikin kundin dokokin yanar gizo, ta ce Sowore ya yi amfani da shafukansa na dandalan sada zumunta na X da Facebook wajen wallafa wani saƙo da ke cin mutuncin Shugaba Tinubu.

Tun dai a farkon watan nan ne DSS ta buƙaci goge wani saƙo da ɗan gwagwarmayar ya wallafa wanda ta riƙa a matsayin bayanan ƙarya, cin zarafi ta yanar gizo da kalaman haddasa ƙiyayya, waɗanda kuma ta ce na iya haddasa rikici su kuma ɓata sunan Najeriya a ƙasashen waje.

Sai dai har zuwa ranar Litinin, 15 ga watan Satumba, babu wani mataki da aka ɗauka na goge saƙon da DSS ɗin ta buƙata.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Malam Madori Ta Horar Da Mata Kare Kai Daga Cututtukan Mahaifa
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
  • An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • Baqa’i: Kowace Kasa A Duniya Tana Da Hakkin Mallakar Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa
  • Sudan ta soki takunkuman da Amurka ta kakaba mata