Sin Ta Mai Da Martani Kan Takardar Bayani a Kan Manufar “Zuba Jari A Amurka Ta Zamanto Farko”
Published: 24th, February 2025 GMT
Mai magana da yawun kwamitin sa kaimi ga cinikayya tsakanin Sin da ketare ya amsa tambaya da manema labarai suka gabatar masa kan takardar bayani a kan manufar “Zuba jari a Amurka ta zamanto farko” a gun taron manema labarai da aka gudanar a jiya Lahadi. Inda ya ce, bangaren masana’antu da kasuwancin Sin na matukar kin yarda da matakin da Amurka ta dauka, wanda ya yi gamin-gambiza da batun tsaron kasa wuri guda, sannan ya yi hannu riga kwata-kwata da tsarin kasuwanci tsakanin kasashen biyu.
Kakakin ya kara da cewa, Amurka ta tsaurara matakan tsaro da nufin fakewa da guzuma ta harbi karsana a kan shigo da jari daga bangaren Sin a fannin kimiyya da manyan ababen rayuwa da kiwon lafiya da aikin gona da makamashi da kayayyakin da ake sarrafawa da sauransu, a hannu guda kuwa, ta yi yunkurin habaka takaita zuba jarinta a kasar Sin ta hanyar daukar matakan sanya takunkumi da tantance harkar kudade da sauransu. Kuma da zarar an aiwatar da matakan da ake dauka, za su kara tagayyara manufofin da kamfanoni za su aiwatar, zai yi matukar illa ga zaman oda da dokar cinikayyar duniya da haifar da rashin tabbaci ga tsarin samar da kayayyaki a duniya.
Kakakin ya ce, “Sin na kalubalantar Amurka da ta mutunta ka’idar kasuwanci da yin takara daidai wa daida, da kuma fahimtar ainihin iyakar batun tsaron kasar da soke kayyade zuba jari tsakanin kasashen biyu ta yadda za a shimfida yanayi mai yakini ga masana’antu da kasuwancin kasahen biyu kan hadin gwiwarsu ta moriyar juna.” (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ganawa A Tsakanin Mataimakan Ministocin Waje Na Kasashen Saudiyya, China Da Minista Arakci Na Iran
Kamfanin dillancin labarun “Mehr” na Iran ya nakalto ganawar da aka yi a tsakanin mataimakan ministocin harkokin waje na kasashen Saudiyya, Walid Khariji, da na China Miao Deo da kuma ministan harkokin wajen Iran Abbas Arakci.
A yayin wannan taron, ministan harkokin wajen Iran ya bayyana gamsuwarsa da yadda kasar China take daukar matakai na gina kyakkyawar alaka a cikin yannacin Asiya, sannan kuma ya bayyana matsayar Iran na bunkasa alakarta da kasashe makwabta.
Ministan harkokin wajen na Iran ya yi Ishara da yadda alaka a tsakanin Tehran da Riaydh take bunkasa a cikin fagage mabanbanta, haka nan kuma yadda suke tuntubar juna akan batutuwan da kasashen biyu suke bai wa muhimmanci.
Haka nan kuma ya yi Ishara da rawar da kasar china ta taka wajen karfafa zaman lafiya a tsakanin kasashen Iran da Saudiyya, da kuma taimakawa a wajen aiki da doka a duniya.
Minista Arakci ya kuma tabo batun alaka a tsakanin Iran da China yana mai kara da cewa, kasashen biyu sun daura aniya fadada wannan alakar.
A nasu gefen, jami’an diplomasiyyar na Saudiyya da China sun yaba wa Iran akan yadda ta karbi bakuncin taron kasashen uku wanda shi ne karo na uku. Haka nan kuma sun nuna azamarsu ta ganin an fadada wannan alakar.
Gabanin wannan ganawar, jami’an diplomasiyyar na China da Saudiyya sun gana da takwaransu na Iran Majid Takht-Ravanchi akan batun karfafa alakar kasashen uku.
Sanarwar ta sake jaddada kudirin Iran da Saudiyya na bin dukkan tanade-tanaden Yarjejeniyar Beijing ta 2023, wanda ya sauwaka wajen dawo da huldar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu a shiga tsakani na China.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Antoni Gutress Ya Yi Allawadai Da Kutsen Da “Isra’ila” Ta Yi A Cibiyar Unrwa December 10, 2025 Iran da Saudiyya sun sake jaddada fadada dangantakarsu December 9, 2025 Faransa ta ce da hannunta aka dakile juyin mulki a Benin December 9, 2025 RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne December 9, 2025 An cire Tony Blair daga jerin wadanda zasu jagoranci Gaza December 9, 2025 Isra’ila ta sake kai hare-haren a kudancin Lebanon December 9, 2025 Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine December 9, 2025 Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba December 9, 2025 Najeriya : Matsala ce ta sa jirgin sojinmu yin saukar gaggawa A Burkina Faso December 9, 2025 Saudiya da Qatar Zasu Gina Layin Dogo Mai Sauri Tsakanin Kasashen Biyu December 9, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci