HausaTv:
2025-06-15@08:32:37 GMT

Isra’ila-Hamas: Za’ayi Musayar Fursunonin Karshe Karkashin Yarjejeniyar Farko

Published: 22nd, February 2025 GMT

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas, ta ca zata saki ‘yan Isra’ila shida yau Asabar a matakin karshe na yarjejeniyar tsagaita wuta ta farko da ta cimma da Isar’ila.

An kuma tsara Isra’ila za ta saki fursunonin falasdinawa Falasdinawa 602 a wannan Asabar a musayar wacce ita ce ta bakwai tun cimma yarjejeniyar a ranar 19 ga watan Janairu tsakanin Isra’ila da Hamas.

Tun dai bayan cimma yarjejeniyar Hamas ta saki Isra’ilawa 22, a yayin da ita kuwa Isra’ila ta saki fursunonin Falasdinawa sama da 1,100.

A karshen matakin farko na yarjejeniyar tsagaita bude wuta, za a yi musayar fursunonin Falasdinawa 1,900 da aka yi garkuwa da ‘yan Isra’ila  su 33 da suka hada da matattu takwas.

Ana dai ci gaba da tattaunawa kan mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wutar tsakanin bangarorin biyu a yayin da dukkansu ke zargin juna da keta yarjejeyar.

Shugaban ofishin yada labarai na gwamnati a Gaza ya sanar da cewa sau fiyesama da 350 Isra’ila ta keta yarjejeniyar tsagaita da Isra’ila ta cim ma a ranar 15 ga watan Janairu.

Tun bayan sanya hannu kan yarjejeniyar tsagaita wuta, sojojin Isra’ila sun kashe tare da raunata Falasdinawa da dama ta hanyar hare-hare ta sama da suka hada da jiragen yaki da jirage marasa matuka, da harbe-harbe kai tsaye.

Sauran laifukan sun hada da kutsen da Isra’ila ta yi a yankunan kan iyaka da ke gabashin Gaza.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: yarjejeniyar tsagaita Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai

Wasu Hare-haren da gwamnatin Isra’ila ta kai ya haddasa gobara a wasu matatun mai a lardin Bushehr da ke kudancin kasar Iran.

Gobarar ta tashi ne a wurin a ranar Asabar bayan da wasu kananan jiragen yakin Isra’ila guda biyu suka kai hare-hare a kan kayayyakin sarrafa iskar gas da ke yankin kudancin Pars.

Hare-haren sun yi haddassa fashe fashe a matatar iskar gas ta Fajr-e Jam, daya daga cikin mafi girma a Iran, da kuma wata karamar matatar mai a mataki na 14 na tashar iskar gas ta Kudu Pars.

Har yanzu ba a fitar da kiyasin barnar a hukumance ba.

Bayan gobarar, ma’aikatar mai ta Iran ta fitar da wata sanarwa inda ta tabbatar da harin.

Sanarwar ta ce, nan da nan aka kaddamar da aikin shawo kan gobarar da dakile ta.”

Matatar man ta Pars ta kudu ita ce tashar iskar gas mafi girma a duniya, wacce ke kan iyakar teku tsakanin Iran da Qatar.

Ta kunshi sama da kashi 70% na bukatun iskar gas na Iran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
  • Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya
  • Hamas : Ziyarar ministan Isra’ila Ben-Gvir a masallacin al-Aqsa kan iya tayar da yakin addini
  • Babu wanda ya tsira daga hatsarin Jirgin Air India mai dauke da fasinjoji 242