HausaTv:
2025-09-17@23:15:41 GMT

Isra’ila-Hamas: Za’ayi Musayar Fursunonin Karshe Karkashin Yarjejeniyar Farko

Published: 22nd, February 2025 GMT

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas, ta ca zata saki ‘yan Isra’ila shida yau Asabar a matakin karshe na yarjejeniyar tsagaita wuta ta farko da ta cimma da Isar’ila.

An kuma tsara Isra’ila za ta saki fursunonin falasdinawa Falasdinawa 602 a wannan Asabar a musayar wacce ita ce ta bakwai tun cimma yarjejeniyar a ranar 19 ga watan Janairu tsakanin Isra’ila da Hamas.

Tun dai bayan cimma yarjejeniyar Hamas ta saki Isra’ilawa 22, a yayin da ita kuwa Isra’ila ta saki fursunonin Falasdinawa sama da 1,100.

A karshen matakin farko na yarjejeniyar tsagaita bude wuta, za a yi musayar fursunonin Falasdinawa 1,900 da aka yi garkuwa da ‘yan Isra’ila  su 33 da suka hada da matattu takwas.

Ana dai ci gaba da tattaunawa kan mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wutar tsakanin bangarorin biyu a yayin da dukkansu ke zargin juna da keta yarjejeyar.

Shugaban ofishin yada labarai na gwamnati a Gaza ya sanar da cewa sau fiyesama da 350 Isra’ila ta keta yarjejeniyar tsagaita da Isra’ila ta cim ma a ranar 15 ga watan Janairu.

Tun bayan sanya hannu kan yarjejeniyar tsagaita wuta, sojojin Isra’ila sun kashe tare da raunata Falasdinawa da dama ta hanyar hare-hare ta sama da suka hada da jiragen yaki da jirage marasa matuka, da harbe-harbe kai tsaye.

Sauran laifukan sun hada da kutsen da Isra’ila ta yi a yankunan kan iyaka da ke gabashin Gaza.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: yarjejeniyar tsagaita Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Daga ranar 14 zuwa 15 ga wata, an gudanar da sabon zagayen shawarwari kan harkokin tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Amurka a birnin Madrid, babban birnin kasar Spaniya, inda bangarorin biyu suka yi musayar ra’ayoyi a kan harkokin cinikayya da ke janyo hankalinsu, tare da cimma daidaito ta fannin daidaita batutuwan da suka shafi Tiktok, da rage shingayen zuba jari, da sa kaimin hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya a tsakaninsu.

Taron shawarwarin ya kasance zagaye na hudu da sassan biyu suka gudanar cikin watanni biyar da suka wuce. Kwatankwacin shawarwarin da aka gudanar a baya, a karo na farko, an sanya Tiktok cikin batutuwan da aka tattauna a shawarwarin na wannan zagaye. Yadda Sin da Amurka suka cimma daidaito a kan batun, ya kuma sake shaida cewa, samun moriyar juna shi ne tushen huldar kasashen biyu ta fannin tattalin arziki da cinikayya.

Hada karfi da karfe shi ne mafita daya tilo, a yanayin da ake ciki na karancin karfin bunkasuwar tattalin arzikin duniya. Ba za a rasa samun sabanin ta fannin tattalin arziki da cinikayya a tsakanin Sin da Amurka ba, amma duk da haka, akwai mafita idan sun dinga yin shawarwari da juna. A gaba, ya kamata sassan biyu su tabbatar da daidaito da shugabannin kasashen biyu suka cimma, musamman ma ya kamata Amurka ta samar da yanayin kasuwanci mai adalci ga kamfanonin kasar Sin, ciki har da Tiktok, kuma ta yi hadin gwiwa da kasar Sin, don su kiyaye nasarorin da suka cimma a shawarwarin, don tabbatar da hada-hadar tattalin arziki da cinikayya a tsakaninsu yadda ya kamata. (Lubabatu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 
  • Hukumar Tarayyar Turai Ta Gabatar Da Shawarar Jingine Aiki Da Yarjejeniyar KAsuwanci Da HKI
  •  Gaza: HKI Tana Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa  Kisan Kiyashi A Gaza
  • Hamas Ta Karyata Gwamnatin Mamayar Isra’ila Kan Shirga Karya Don Kare Muggan Manufofinta
  • Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA
  • Hamas ta bukaci kasashen musulmi da na Larabawa su dauki mataki mai tsari kan Isra’ila