Rundunar Sojojin Qassam Ta Tabbatar Da Kashe Wani Jami’anta A Lebanon
Published: 17th, February 2025 GMT
Bangaren kungiyar Hamas da ke dauke da makamai ya tabbatar da shahadar wani daga cikin jami’in kungiyar a wani harin Isra’ila.
Muhammad Ibrahim Shaheen, ya yi shahada ne a wani harin da wani jirgin yakin Isra’ila ya kai a Sidon.
Kassam Brigades ta bayyana shi a matsayin wanda ya yi tsayin daka kan zalincin Isra’ila, ciki har da lokacin yakin Gaza.
Ita ma Isra’ila ta tabbatar da kashe jami’in na Hamas a harin da ta ce ta kai kan a Lebanon
Sojojin Isra’ila sun yi ikirarin kai harin ta sama a Sidon, inda suka ce sun kashe wani “dan ta’adda” Bafalasdine.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake ta kokarin ganin yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma tsakanin Isra’ila da Hamas ta daure.
Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya fada jiya Lahadi cewa, tawagar tattaunawa ta kasar za ta je birnin Alkahira domin tattaunawa kan aiwatar da yarjejeniyar.
Sanarwar ta kara da cewa, da farko dai tawagar za ta fara tattaunawa ce kan ci gaba da aiwatar da mataki na daya na yarjejeniyar tsagaita wutar, kana za a ba ta umarni a kan ci gaba da tattaunawa game da kashi na biyu, bayan taron majalisar tsaron Isra’ila.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa
Ya mika saƙon ta’aziyyarsa Kwamishinan ‘Yansandan Jihar, Shetima Jauro Mohammed, ga iyalan mamacin tare da tabbatar da cewa an ƙaddamar da bincike mai zurfi tare da shiga farautar waɗanda suka aikata harin domin a cafke su.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp