HausaTv:
2025-07-13@11:30:54 GMT

Rundunar Sojojin Qassam Ta Tabbatar Da Kashe Wani Jami’anta A Lebanon

Published: 17th, February 2025 GMT

Bangaren kungiyar Hamas da ke dauke da makamai ya tabbatar da shahadar wani daga cikin jami’in kungiyar a wani harin Isra’ila.

Muhammad Ibrahim Shaheen, ya yi shahada ne a wani harin da wani jirgin yakin Isra’ila ya kai a Sidon.

Kassam Brigades ta bayyana shi  a matsayin wanda ya yi tsayin daka kan zalincin Isra’ila, ciki har da lokacin yakin Gaza.

Ita ma Isra’ila ta tabbatar da kashe jami’in na Hamas a harin da ta ce ta kai kan a Lebanon

Sojojin Isra’ila sun yi ikirarin kai harin ta sama a Sidon, inda suka ce sun kashe wani “dan ta’adda” Bafalasdine.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake ta kokarin ganin yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma tsakanin Isra’ila da Hamas ta daure.

Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya fada jiya Lahadi cewa, tawagar tattaunawa ta kasar za ta je birnin Alkahira domin tattaunawa kan aiwatar da yarjejeniyar.

Sanarwar ta kara da cewa, da farko dai tawagar za ta fara tattaunawa ce kan ci gaba da aiwatar da mataki na daya na yarjejeniyar tsagaita wutar, kana za a ba ta umarni a kan ci gaba da tattaunawa game da kashi na biyu, bayan taron majalisar tsaron Isra’ila.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

Ya mika saƙon ta’aziyyarsa Kwamishinan ‘Yansandan Jihar, Shetima Jauro Mohammed, ga iyalan mamacin tare da tabbatar da cewa an ƙaddamar da bincike mai zurfi tare da shiga farautar waɗanda suka aikata harin domin a cafke su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Sun Kama ‘Yan Leken Asirin Isra’ila A Lardin Mazandaran Na Kasar Iran
  • Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
  • An Kashe Jami’in Sojan HKI A Gaza
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa
  • Kamfanonin Jiragen Ruwa Sun Yanke Hulda Da Isra’ila Saboda Matsalar Hare-Haren Kasar Yemen
  • HKI Ta Ci Gaba Da Kai Hare-Hare Kan Kudancin Kasar Lebanon
  • Sojoji sun kashe ’yan fashin daji masu yawan gaske a Zamfara
  •  Masu Kare Hakkin Dan’adam Suna Allawadai Da Takunkumin Amurka  Akann Jami’ar MDD A Falasdinu
  • Somaliya: Kungiyar Al-Shabab Ta Kai Wa Barikin Soja Hari A Birnin Magadishu
  • Sojoji sun tarwatsa matsugunin ’yan ta’adda da kashe wasu a Borno