HausaTv:
2025-05-28@03:56:48 GMT

Rundunar Sojojin Qassam Ta Tabbatar Da Kashe Wani Jami’anta A Lebanon

Published: 17th, February 2025 GMT

Bangaren kungiyar Hamas da ke dauke da makamai ya tabbatar da shahadar wani daga cikin jami’in kungiyar a wani harin Isra’ila.

Muhammad Ibrahim Shaheen, ya yi shahada ne a wani harin da wani jirgin yakin Isra’ila ya kai a Sidon.

Kassam Brigades ta bayyana shi  a matsayin wanda ya yi tsayin daka kan zalincin Isra’ila, ciki har da lokacin yakin Gaza.

Ita ma Isra’ila ta tabbatar da kashe jami’in na Hamas a harin da ta ce ta kai kan a Lebanon

Sojojin Isra’ila sun yi ikirarin kai harin ta sama a Sidon, inda suka ce sun kashe wani “dan ta’adda” Bafalasdine.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake ta kokarin ganin yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma tsakanin Isra’ila da Hamas ta daure.

Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya fada jiya Lahadi cewa, tawagar tattaunawa ta kasar za ta je birnin Alkahira domin tattaunawa kan aiwatar da yarjejeniyar.

Sanarwar ta kara da cewa, da farko dai tawagar za ta fara tattaunawa ce kan ci gaba da aiwatar da mataki na daya na yarjejeniyar tsagaita wutar, kana za a ba ta umarni a kan ci gaba da tattaunawa game da kashi na biyu, bayan taron majalisar tsaron Isra’ila.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gaza : Spain ta bukaci kasashen duniya su kakabawa Isra’ila takunkumi

Kasar Spain ta bukaci kasashen duniya dasu kakabawa Isra’ila taklunkumi saboda ci gaba da yin fatali da kiraye-kirayen da ake matana tadakatar da yakin da take a Gaza.

Ministan harkokin wajen Spain José Manuel Albares ya ce kamata ya yi kasashen duniya su kakabawa Isra’ila takunkumi domin kawo karshen munanan hare-haren soji a zirin Gaza da aka yi wa kawanya.

Shugaban diflomasiyyar Spain yana magana ne gabanin wani babban taron kasashen Turai da na Larabawa da za a yi ranar Lahadi a Madrid.

“Dole ne mu komai, don kawo karshen wannan yakin,” in ji shi.

M.Albares ya bukaci a shigar da agajin jin kai, ba tare da wani sharadi ba, ba tare da tsangwama ba, ta yadda Isra’ila ba ta yanke shawarar wanda zai iya ci da wanda ba zai iya ba.

Taron na ranar Lahadi, wanda ya hada da wakilan kungiyar hadin kan kasashen Larabawa da kungiyar hadin kan kasashen musulmi, na da nufin ingiza bukatar da wasu kasashen duniya ke mikawa  na samar da kasashe biyu da bufin kawo karshen rikicin da aka kwashe shekaru anayi.

Isra’ila dai na fuskantar matsin lamba daga kasashen duniya, musamman daga kawayenta na kut-da-kut kan ta dakatar da kai hare-haren da take kaiwa da kuma ba da damar kai agajin jin kai a Gaza.

A wannan makon ne Tarayyar Turai ta kada kuri’ar amincewa da sake duba yarjejeniyar kungiyar da Isra’ila.

A halin da ake ciki kuma, a baya-bayan nan kasar Sweden ta ce za ta matsa wa kungiyar mai kasashe 27 lamba kan ta kakaba takunkumi kan ministocin Isra’ila, yayin da Birtaniyya ta dakatar da tattaunawar cinikayya cikin ‘yanci da Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Yahudawa sun Kashe Wani Matashi A Yankin Yamma Da Kogin  Jordan
  • Rundunar Ƴansanda Ta Gayyaci Jami’anta Da Bidiyonu Ya Yaɗu Suna Karɓar Cin Hancin Naira 5000
  • Wani abu ya fashe kusa da barikin soji a Abuja
  • ‘Yansanda Sun Nemi A Kwantar Da Hankula Bayan Fashewar Wani Abu A Abuja
  • Gaza : Spain ta bukaci kasashen duniya su kakabawa Isra’ila takunkumi
  • Falasdinawa 30 sun yi shahada a Wani harin Isra’ila kan wata makaranta
  •  Sojojin HKI Sun Yi Wani Sabon Kisan Kiyashi A Gaza
  • Ana zargin wani mutum da kashe ɗan maƙwabtansa a Sakkwato
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Suna Ci Gaba Da Kai Hare-Haren Wuce Gona Da Iri Kan Birnin Tul-Karam Na Falasdinu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 5 A Katsina