An Bude Babban Taron Kasa Na Nijar
Published: 15th, February 2025 GMT
A Nijar yau ne aka bude babban taron kasar, wanda zai tsara dokoki kan yadda za’a tafiyar da kasar a lokacin mulkin rikon kwarya na soji.
Shugaban Nijar Janar Abdourahamane Tiani ne ya kaddamar da taron a Yamai babban birnin kasar inda ake sa ran shafe kwanaki hudu ana tattaunawa.
Taron zai kuma bayar da shawara kan tsawon wa’adin gwamnatin rikon kwarya.
Taron ya samu halartar tsofaffin shugabannin kasar ciki har da Mahamadou Issoufou da tsofaffin shugabannin majalisar dokokin kasar da tsofaffin firaministoci na kasar da wasu baki daga Burkina Faso da Mali da wasu kasashen.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
Rahoton rashin fahimtar da aka fara yadawar, ya biyo bayan taron kwamitin zaman lafiya da kwantar da tarzoma na jihar, wanda Darakta Janar ya jagoranta a ranar 4 ga watan Satumba.
Rashin fahimtar sahihin sakamakon taron ya sa wasu suka rahoto cewa, kwamitin ya dakatar da Malamai daga yin wa’azi.
Sanarwar ta kara da cewa, “Hukumar ba ta da hurumin haramtawa Malaman Addinin Musulunci yin wa’azi sai dai in ya bayyana a fili an taka ƙa’idojin hukumar da ta shimfiɗa”.
A cewar Hukumar, an kira taron ne domin gabatar da fom din rijistar yin wa’azi ko Da’awah da kuma bin tsarin tantancewa.
Ta bayyana shirin a matsayin wani yunkuri na wayar da kan jama’a don “hana rashin fahimtar juna da kuma daƙile yaɗuwar wa’azin yaudara” a faɗin jihar Neja.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp