NUJ Ta Dukufa Wajen Kula Da Jin Dadin ‘Yan Jarida
Published: 14th, February 2025 GMT
Kungiyar ‘yan jarida ta Najeriya (NUJ) karkashin jagorancin shugaban kasa Alhassan Yahaya, ta jaddada aniyar ta na inganta aikin jarida da kuma jin dadin ‘yan jarida a fadin Najeriya.
Kungiyar tana aiki tukuru don ganin an zartar da kudurin dokar inganta kafafen yada labarai a majalisar dokokin kasar don karfafa masana’antar.
A cikin sanarwar da ta fitar a karshen taron kaddamar da kwamitin koli (CWC), wanda aka gudanar a Birnin Kebbi, Jihar Kebbi, kungiyar na hada kai da Majalisar Dokoki ta kasa, kungiyoyin farar hula, da sauran masu ruwa da tsaki domin ganin an samar da dokar inganta harkokin yada labarai.
Sanarwar ta bayyana cewa, CWC ta yanke shawarar gano harkokin kasuwanci don samun kudaden shiga don tabbatar da tafiyar da harkokin kungiyar cikin sauki.
Har ila yau, ta ce, mambobin CWC sun yaba wa shugaban NUJ bisa hangen nesansa kuma sun bukace shi da ya ci gaba da ci gaba da ciyar da manufofin kungiyar gaba.
Sanarwar ta yi bayanin cewa, kungiyar za ta shirya taron karawa juna sani na horar da ‘yan jarida guda biyu a cikin rubu’in farko na shekara don bunkasa sana’o’i a bangarori daban-daban na harkar yada labarai.
Domin tabbatar da gaskiya wajen fitar da kudaden rajista, kungiyar na tattaunawa da ofishin biyan albashi na zamani na tarayya (IPPIS) domin tabbatar da cewa duk kudaden da aka cire daga mambobin kungiyar NUJ ana tura su kai tsaye zuwa asusun NUJ.
CWC ta yabawa gwamnatin jihar Kebbi kan ci gaban ababen more rayuwa da suka hada da titunan gari, filin ajiye motoci na zamani, zuba jarin noma, da tsare-tsare na jin dadin jama’a, ya kuma bukaci gwamnan da ya ci gaba da gudanar da wannan kokari na ganin ya cika aikin da ya rataya a wuyansa a matsayinsa na dan kungiya.
Kungiyar ta NUJ ta bukaci Gwamnatin Tarayya da ta yi amfani da fadin kasar nan na noma domin bunkasa samar da abinci sannan kuma ta yi kira ga hukumomin tsaro da su kara kaimi wajen magance kalubalen tsaron da ke addabar al’ummar kasar, haka ma gwamnati ta ba da fifikon jin dadin ‘yan kasa wajen tsara manufofi.
PR/Abdullahi Tukur/Wababe
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250 a Jami’ar Ilorin
Babban attajirin Afirka kuma Shugaban Rukunin Kamfanin Dangote, Alhaji Aliko Ɗangote, ya ɗauki nauyin gina ɗakunan kwanan ɗalibai masu gadaje 250 da Babban Masallacin Juma’a na Ilorin ya tsara a Jami’ar Ilorin da ke Jihar Kwara.
An kiyasta aikin zai ci kusan naira biliyan 1.1, kuma an ƙaddamar da shi ne domin samar da hanyar samun kuɗin kula da masallacin.
Ana sa ran kuɗaɗen haya da za a samu daga ɗaliban da za su zauna a wurin zai rika shiga asusun kula da masallacin.
Sakataren kwamitin amintattu na masallacin, Alhaji Shehu AbdulGafar, ya shaida wa manema labarai a Ilorin cewa Ɗangote ya riga ya sanar da su cewa zai ɗauki nauyin aikin gaba ɗaya.
Cire tallafin man fetur shi ne abin da ya dace —Sarki Sanusi II NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar RuwaYa ce an riga an rattaba hannu kan yarjejeniya da Jami’ar Ilorin wadda ta ba wa masallacin damar mallaka da gudanar da ɗakin kwanan ɗaliban na tsawon shekaru 21 kafin a miƙa shi ga jami’ar.
Baya ga aikin ginin, Ɗangote ya kuma yi alƙawarin bayar da tallafin Naira miliyan 5 a kowane wata domin kula da masallacin har sai an kammala aikin.
AbdulGafar ya ce wannan taimako zai rage nauyin kuɗin aikin, tare da tabbatar da ɗorewar ayyukan masallacin.
Ya ƙara da cewa ɗakin kwanan zai taimaka wajen rage matsalar ƙarancin wurin kwana ga ɗaliban jami’ar.
Shugabannin al’umma da sauran masu ruwa da tsaki sun yaba wa Ɗangote, sun bayyana wannan mataki a matsayin abin koyi na yadda za a iya haɗa kai tsakanin cibiyoyin addini da ’yan kasuwa wajen ci-gaban al’umma.