Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Hassan (s) 11
Published: 2nd, February 2025 GMT
11-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da war haka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshi wadanda suka zo cikin alkur’ani mai girma, ko cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane rastan na Aya. Shahida Murtada Muttahari, ko kuma cikin littafin Mathnawi na maulana Jalaluddin rumi.
///..Madallah, masu sauraro idan kuna tare da mu a shikin shirimmu da ya gabata, mun ci gaba da kawo maku sirar Imam Hassan (a) jikan manzon All..(s) kuma limami na biyu daga cikin limamai masu tsarki daga cikin iyalan gidan manzon All..(s), sannan dan Fatimah(a) diyar manzon All..(s) na farko.
Masu sauraro a cikin shirimmu da ya gabata, mun bayyana cewa, Manzon All..(s) ya isar da manzancon ne a ranar Ghadir shekara ta 10 bayan hijira a wani wurin da ake kira Ghadir Khom dake tsakanin Makka da Juffa, wannan sanen nen wuri wanda ya kasance mikati ga mutanen Makka da kewaye. Inda ya nada Aliyu dan Abitalib (a) a matsayin Khalifansa, kuma wanda zai jagoranci al-ummarsa zuwa tudun na tsira a nan duniya da kuma Lahira. Sai dai al-umma ta yi watsi da su sun kuma kafirwa ni’imar da Al..ya yi masu.
Don haka sai All..ya mai da kungiyoyi suna yakar juna, ko wace kungiya tana alfahiri da abinda ya tara na mutane, yana kuma riye cewa su kadai ne suka kan gaskiya.
Mun ji yadda Imam Hassan (a) ya kafa hujja da ayar Ghadir ya kuma bayyana cewa bayan saukar ayar ne kakansa ya kama hannun mahaifinsa ya daga hannun babansa ya kuma ce duk wanda ni shugabansa ne to Aliyu shugabansa ne . Ya ubangiji ka jibance wanda ya jibance shu ka tabar da wanda ya tabar da shi.
Daga krashen mun ji Imam Hassan (a) ya fada masu cewa sun ji manzon All…(s), ko kakanda yana fadawa babana kan cewa: Matsayina da kai kamar matsayin Haruna da musa be sai babu annabci a bayana.
Hakika littafan tarihi suna dauke da wasu abubuwa da dama dangane da hadisin Ghadir da kuma yadda limamai daga iyalan gidan manzon All..(s) da malamansu suka yi ta kafa hujja da shi a tsawon tarihi.
Ammam al-ummar ta zabi wani abu daban ta kuma zabauwa kanta sabanin haka bayan ta fahinci abinda hadisin Ghadir ya kunsa.
Sannan bayan komawar Madina daga aikin hajji, manzon All..ya zauna wasu kwanaki sai aka umurceshi ya yiwa ma’abuta kaburbura a Baki’a. Sai ya kira Abu Mauhiban, wanda ya kasance maulansa ne wanda ya saye shi kuma yentar da shi, a lokacinda yazo a cikin dare, sai yace masa an umurce ni in yiwa mutanen makabartan baki’a istigfari, ina son ka rakani, sai Abu muhiba ya rakashi zuwa Baki’a inda ya tsaya ya kuma yi masu istigfari kamar yadda aka umurce shi.
Da farko ya yi sallama ga mamata da suke makabartan, sannan , ya kuma ce masu, kunji dadi da halin da suke ciki, Daga nan sai ya fara bada labarin bakar fitina wacce zata fadawa al-ummarsa a bayansa.
Sai ya fara addu’a yana cewa: Amincen All..su tabbata a gareku ya ku ma’abuta kaburbura, Lalle ku ina maku murna kan halin da kuke ciki, idan an kwatanta da halin da mutanen suke ciki a halin yanzu. Hakika fitinu kamar bangarorin duhun dare yana kan hanyar zuwa cikinsu, sun bin juja, duk wanda yazo daga baya sai yafi muni kan wanda ya zo gabaninta.).
A lokacinda Abu Mauhiban ya ji addu’ar manzon All..(s) da kuma abinda yayi magana na gabatowar fitina, sai ya fara gurin ina ma da ace ya mutu. Sai manzon All..(s) ya ce masa: Lalle ni an bani mabudan taskokin duniya da dawwa a cikinta sannan Aljanna, sai na zabi haduwa da Ubangiji na, sannan Aljanna.)
Sai Abu Mauhiban ya ce masa: Iyaye na fansarka shin ba zata karbi mabudan taskar duniya ka dawwa a cikinta sannan Aljanna bayan haka ba?
Sai manzon All..(s) ya fada masa bukatarsa mai tsanani na haduwarsa da All.. sai yace masa{ Babu wallahi na zabi haduwata da All..) sannan ya nemi gafara ga ma’abuta makabartan Baki’a sannan ya juya ya koma gida.
A lokacinda manzon All..ya ga alamun wafati a kusan zuwa, sai yana son ya karfafa Aliyu (a) al-amarinsa a bayansa, sai ya tarawa Usama dan Zaidu runduna, wanda hakan zai nisantar da dukkan wadanda suke kodayin khalifanci daga madina a lokacinda zai yi wafati, sannan Amirul mumina(a) zai karbi jagoranci ba tare da wata matsala ba.
Don haka ya hada runduna karkashin jagorancin Usuma dan zaidu, sannan ya tura dukkan wadanda yake da tabbacin cewa suna kodayin khalifanci a bayansa su fita yaki tare da Usama dan zaidu. Manzon All..(s) ya tura tare da Usama, dukkan manya-,manyan sahabbai daga ciki har da Abubakar da Umar da Uthman da Ubu ubaida dan Jarra, da bashir dan Sa’adu da sauransu.
Ya shugabantar da Usama dan Zaidu a kansu, wanda ya kasance dan shekara 17 a duniya ne.
Manzon All..(s) ya kulla tutar yaki ya bawa Usama dan Zaidu ne kwanaki 4 kafin karshen wata Safar na shekara ta 11 bayana hijira. Sannan ya fadawa Usaman, : Kaje inda aka kashe babanka, ka tattakasu da dawakanka, na shugabantar da kai wannan rundunar.
Ka kai hari kan mutanen ‘Abni” da sassafe, ga gaggauta tafiya saboda kada labarinka zuwarka ya isa kafin ka iso. Idan All..ya baka nasara a kansu ka, kada ka dade a cikinsu. …har zuwa inda yace : ka dauko masu baka labari, ko ta’a ina. Tare da kai, su rika baka labari.
Sai a ranar 28 ga watan Safar, sai rashin lafiyar manzon All..(s) yayi tsanani, kuma zazzabi ya rufe jikinsa. Tare da tsananin ciwon kai. Amma wasu suka ce zazzabin da kuma ciwon kan saboda abinci mai guban da ya ci a baya ne, a yakin Khaibara. Suka ce yana cewa : Har yanzun ban gushe ba anajin dandanon abincin da na ci a khaibara.
A lokacinda gari ya waye, sai ya ga wasu sahabbansa wadanda suka sabawa umrninsa, suna cikin Madina kamar yadda aka bashi labari.
Sai ya sake fita a ranar 29 ga watan safar ya sake kullawa Usama dan Zaidu tuka ya ce masa, ta tafi yaki da izinin All.. kan tafarkin All.., ka yaki kafirai).
Sai usama yak arbi tutan sannan ya mika shi ga Buraidatul Aslami, sannan ya je ya yi sansanin A Jurf kafin sauran mutane su taru su tafi da shi.
Sai mutanen sun yi ta jan kafa, sun ki fita tare da shi suna, jinkiri sosai, sai Umar ya fadawa Usama: Manzon All..(s) ya mutu kana a matsayin shugaba na?.
Sai suka fara yin korafi kan shugabantar da Usaba a kansu, musamman ganin cewa su, dattawa ne masu fararen geme, sannan usama kuma dan zaidu na Haritha ne wanda ya kasance yentaccen bawan manzon All..(s) wanda ya yenta shi.
Don haka sun yi ta jan kafa wajen hadewa da sauran rundunar Usama, kuma maganganunsu ya isa kunnen manzon All..(s).
A lokacinda ya ji sukarsu ga shugabancin Usama da kuma jan kafar da suke yi, sai rashin lafiyarsa ya karu, sannan ciwon kai ya rufe shi, ya kuma yi bakin ciki sosai kan hakan. Sai ya fito yana daure da kansa da wani kelle, yana kuma jin tsoron dabarar da yayi ba zai kai ga nasara ba.
Ya je masallaci ya hau mimbari a ranar 10 ga watan Rabi’ul awwal, ya bayyana bakin cikinsa da rashin tafiyarsu, da kuma sabawa al-amarinsa. Sai ya fara khuba yana cewa :
Ya ku mutane ! wani irin zance ne nake ji daga wajenku, dangane da shugabancin Usama, wallahi idan kunyi suka kan shugabancin Usama, to kun yi suka kan shugabancin babansa a baya, Na rantse da All… lallei ya cancanci shugabanci , kuma babansa ma ya cancance ta.
Sai ya sauka daga membari, ya koma gidansa yana cewa, ku tafi da rundunar Usama, ku aiwatar da rundunar Usama, All..ya la’ani wanda bai je tare da rundunar Usama ba.
Amma dukkan jawabai da kuma maganganinsu dangane da rundunar Usama, shiga zuciyarsu ba. Sai ma sun yi ta gabatar da uzuransu ga manzon All..(s) bayan dukkan maganganu masu zafi da ya fada dangane da rundunar Usama.
Don haka sun yi watsi da dukkan maganganunsa (s) dangane da rundunar Usama. Wanda ya sa Usaba yak asa tafiya. Har abinda ya faru ya faru.
Wanda yayi tunani a cikin abubuwan da suka faru a wancan lokacin zai fahinci wasu al-amura kamar haka.
01-Dagewar manzon All..(s) wajen ganin rundunar Usama ta tafi, hatta a lokacinda yake fama da tsananin rashin lafiya, da kuma la’anar da yayi kan duk wanda ya ki fita tare da rundunar Usaba, ya nuna cewa dabarar da yayi na fitar da dukkan wadanda suke kodayin shugabanci ko khalifanci a bayasa, dubarar ba za ta sami nasara ba. Don zai yi wafati sunan cikin madina. Zasu aiwatar da shirinsu na kwace khalifanci daga hannun Amirulmuminina Aliyu dan Abitalib (a).
02- sun gano cewa idan sun bar Madina, sannan manzon All..(s) ya rasu, babu wanda zai yi maganar Khalifancin manzon All..(s) a lokacin, Amirulmi muminina (a) zai karbi khalifanci da sauki, sannan ko sun dawo ba za su iya yi masa tawaye ba.
03- Manzon All..ya sanya Usama dan zaidu kan shugabancin runduna ne, saboda idan ya dora tsoffi da kuma wadanda suka kashen shuwagabanni a cikinsu, to zasu yi amfani da wannan damar don cimma manufofinsu ta kodiyan khalifanci a bayansa.
Amma usama matashin ne, idan sun ce Aliyu matashi ne to Usama ma matashi ne.
Da wasu dalilai a dama.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: da rundunar Usama wanda ya kasance wadanda suka masu sauraro Sai ya fara sai ya fara
এছাড়াও পড়ুন:
Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya
Babu abin da ya rage yanzu, illa babatun zantukan siyasa da ‘yan siyasar ke ta fama yi a kasar, wadanda suka jarabtu da matukar son mulki. Wannan abu da ke faruwa yanzu, ko shakka babu zai canja, zai canja din ne kuwa yayin da ‘yan siyasar ke aiwatar da tsare-tsarensu, sai masu jefa kuri’u a Nijeriya kuma su yanke hukunci. Shekarar 2027, za ta kasance mai ban mamaki tare da kalubale ga ‘yan Nijeriya.
A bisa dukkan alamu, jam’iyyar APC ta dukufa wajen kara habaka karfinta ne kawai da ganimar ‘yan adawa. Tana ta faman sa kanta cikin rigingimu, har wadanda ba su shafe ta ba a cikin shekaru biyun da ya rage mata ta yi gaba na kunci da tsanani. Maimakon gwamnatin ta mayar da hankali kan nauye-nauyen da ke kanta, na yi wa al’ummar kasa aiki; sai ta buge da yin fada da jam’iyyar adawa, kullum cikin wasa wukarta; a gefe guda kuma gazawar gwamnatin na fitowa fili.
Kura-kuren gwamnatin sun hada da; girman kai wajen tafiyar da al’amuranta, rashin tafiyar da abubuwa yadda ya kamata; tunanin cewa, jawo ‘yan adawa zai ba ta dama tare da karfin yin fada da kuma lashe zabe; ta hanyar zaben shugaban kasa cikin sauki, wanda kowane bangare zai bayar da gudunmawarsa. Amma, babbar matsalar ita ce; shugaban kasar ba shi da kima a kusan dukkanin sassan kasar.
Jam’iyya mai mulki, za ta iya bunkasa damar da take da ita, idan ba ta tsayar da Tinubu a 2027 ba, musamman idan za ta tsayar da matashi, lafiyayye, dan siyasa mai gaskiya da son ci gaba. Hakan kuwa, da alamu ba zai yiwu ba, domin Tinubu shi ne ked a wuka da nama a jam’iyyar.
Shugaban kasa da kansa, ba zai iya bayar da shawarar yadda za a yi gyara ta hanyar kawo wani dan takarar da ya dace ba. Idan Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, zai kasance a matsayin dan takara, APC za ta yi amfani da dukkanin damammakin da take das u, musamman na amfani da kudi wajen sayen kuri’u da masu zabe. Rage Muslman Arewa saboda Kiristocin Arewa, na iya zama hadari, amma wannan shi ne kawai abin da za a iya yi.
Haka zalika, jam’iyyar ta zama dakikiyar daliba, domin babu abin da take karantawa illa yadda za ta samu damammaki iri daban-daban na siyasa kadai. Dandazon da ‘yan siyasa suka yi a cikinta, ba karamar barazana ba ce ga masu bukatu daban-daban, musamman idan aka kasa biya musu bukatunsu.
Ko shakka babu, Arewa za ta yi matukar tasiri a zaben da za a yi. Shi ne yankin day a fuskantar ayyukan ta’addanci da kuma mummunan talauci da ke biye da su har zuwa rumfunansu na zabe. Saboda haka, dole ne jam’iyyar ta yi aiki tukur don kaucewa sake faruwar zaben 2015, lokacin da jam’iyya mai mulki ta fuskanci daukacin yankin da suka yi mata zanga-zanga.
Kudu-maso-yamma, za su iya goyon bayansa idan ya kasance manyan ‘yan adawa sun fitar da wani dan takarar daga Arewa, amma wannan rashin kwanciyar hankali da ake fama das hi, ya kamata a ce ya hana kowa barci.
Tasirin Wike, zai iya raunanawa ko karfafawa; ya danganta da matakin da ‘yan adawa suka dauka game da rikice-rikice a Kudu-maso-kudu, wanda zai iya daidai da bukatunsu; ba abubuwan da suka dace ba. Za a lalata jam’iyyar LP ba tare da Obi ba, a kuma matse shi a matsayinsa na dan takararta.
Burin Obi yanzu, ya wuce batun jam’iyyar LP; amma akwai barazanar samun raguwa a matsayinsa na dan siyasa, idan ya yanke shawarar da za ta iya raba mabiyansa. Kudu-maso-gabas, sun kagu su ga sun samu mukamin shugabancin kasa, wanda hakan ke nuna kishinta na samun daidaito. Hakan, na iya yiwuwa ta hanyar samun daidaito, ana iya samun hakan ta hanyar yarjejeniya a tsakanin yankunan da ake da su.
Da alamu dai, tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ne ke da babbar matsala. Ya yi rauni da yawa da zai iya ja da bukatar Tinubu na neman wa’adi na biyu. Don haka, sake barin jam’iyyar PDP tare da neman wata jam’iyyar daban, hanya ce kawai ta kasha makudan kudade da bata lokaci da sauran makamantansu.
PDP a halin yanzu, na zub da jini ne sakamakon zagon kasan da jam’iyya mai mulki ke yi mata. Babbar kadararta shi ne Atiku, amma kuma shi ne babbar matsalarta. Matsayinsa na farko a jam’iyyar, shi ne ke haifar da korafe-korafe da rudani, zai yi wuya PDP tare da Atiku su shiga yarjejeniyar da za ta bayar da dama a karo na biyu.
Idan da PDP za ta iya gyaruwa ta samu nasara a kan APC, dab a ta damu da neman biyan bukatun da suka fi muni ko kawo rudani ba. Jam’iyyar da ta taba yi wa al’ummar kasar barazana, yanzu kuma tana cikin sadar kafa tarihi wajen rubuta ta a matsayin wacce da fi bayar da gudunmawa wajen samun nasarar APC 2027.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp