Leadership News Hausa:
2025-09-18@10:19:14 GMT

Gwamnan Kaduna Ya Kare Shirinsa Na Sulhu Da ‘Yan Bindiga

Published: 31st, January 2025 GMT

Gwamnan Kaduna Ya Kare Shirinsa Na Sulhu Da ‘Yan Bindiga

“Da na tambaye shi dalili, sai ya ce al’ummominmu suna fama da barnar ‘yan bindiga da hakan ke janyo asarar rayuka da garkuwa da mutanenmu tsawon shekaru zuwa yanzu ba tare da samun mafita da shawo kan lamarin ba.”

Gwamnan ya ce bayan rokon, ya zauna da masu ruwa da tsaki ciki har da mashawarcin shugaban kasa kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, kafin daga karshe suka amince da fito da shirin yin sulhun.

Ya kara da cewa matakin na zuwa ne bayan da ‘yan fashin dajin suka sako mutane 200 da suka yi garkuwa da su a kananan hukumomin Giwa da Birnin Gwari. Gwamnan ya nuna fatansa na cewa matakin zai dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar ta yadda manoma za su sami damar komawa gonakansu domin yin noma da kuma dawo da harkokin kasuwanci yadda ya kamata.

“Gara na yi sulhu da ‘yan bindiga da ran mutum daya ya salwanta. Idan ba haka ba, ni ne zan je gaban Allah na yi bayanin wannan rasa ran domin na rantse cewa zan kare rayukan mutane,” ya shaida.

Kazalika, ita ma kungiyar Dattawan Arewa (ACF), ta shelanta cikakken goyon bayanta ga matakin Gwamna Uba Sani na yin sulhu da zaman lafiya da ‘yan bindigan a Kaduna da ma yankunanta.

A hirar da ya yi ta wayar salula da LEADERSHIP, jami’in watsa labarai na kungiyar ACF, Farfesa T.A Muhammad Baba, ya ce kungiyar ta yi maraba da yunkurin gwamnan na kawo karshen garkuwa da mutane da aikace-aikacen ‘yan fashin daji.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Fasahar AI ta gano cutar da za ta kama mutane a shekara 10 masu zuwa

Masu bincike a Turai sun yi amfani da fasahar ƙirƙirariyyar basira ta AI don yin hasashen matsalolin lafiya da ɗaiɗaikun mutane za su iya fuskanta cikin shekaru goma masu zuwa ko fiye na rayuwarsu.

Sun ce fasahar na amfanin da bayanan rashin lafiyar da mutum ya yi a baya, domin hasashen cutuka fiye da dubu ɗaya da ke barazanar kama mutum, tun ma kafin soma bayyana.

An wallafa cikakkun bayanan binciken – da suka bayyana da gagarumar nasara – a mujallar kiwon lafiya ta Nature.

An horar da fasahar AI ɗin ta hanyar amfani da bayanan lafiyar mutane dubu ɗari huɗu – da ba a bayyana sunayensu ba – a Birtaniya da Denmark.

Zuwa yanzu ba a soma amfani da fasahar ba, sai dai ana sa ran yin amfani da ita wajen gano cutuka da wuri a mutanen da suka fi barazanar kamuwa da cutuka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fasahar AI ta gano cutar da za ta kama mutane a shekara 10 masu zuwa
  • Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Jajantawa Al’ummar Gumi
  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  • Kungiyar Human Rights Watch; Isra’ila Ta Kashe ‘Yan Jarida Fiye Da 30 A Kasar Yemen Ne Da Gangan  
  • Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi