EFCC ta cafke tsohon shugaban NHIS, Usman Yusuf a Abuja
Published: 30th, January 2025 GMT
Jami’an Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC), sun cafke Tsohon Shugaban Hukumar Inshorar Lafiya ta Ƙasa (NHIS), Farfesa Usman Yusuf, bayan kai sumame a gidansa da ke Abuja.
Aminiya ta tabbatar da cewa jami’an EFCC ɗauke da makamai sun isa gidansa da misalin ƙarfe 4:46 na yammacin ranar Laraba, inda suka kama shi a gaban matarsa da ’ya’yansa.
Sai dai har yanzu ba su bayyana dalilin cafke shi ba.
Wata majiya ta bayyana cewa an kama tare da tafiya da Farfesa Yusuf zuwa wani waje da ba a bayyana ba.
Duk da cewa hukumomi ba su fitar da sanarwa kan tuhumar da ake yi masa ba, wasu majiyoyi sun ce kamun nasa yana da alaƙa da shugabancin da ya yi a hukumar NHIS.
Wani babban jami’in EFCC ya ce, “Ba za a iya bayyana dalilin kama shi a yanzu ba saboda har yanzu ana bincike.
“Amma yana hannunmu kuma zai taimaka wajen gudanar da bincike.”
An cire Yusuf daga muƙaminsa a shekarar 2019 a lokacin mulkin tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari.
Wani kwamitin bincike na Ma’aikatar Lafiya ne, ya bayar da shawarar korarsa bisa zargin ɓatan-dabon Naira miliyan 919.
Da aka tuntuɓi kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya ce zai bincika batun sannan ya yi ƙarin haske daga baya.
Sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, bai yi martani ba.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
Ma’aikatar Gona da tsaron abinci ta ƙasa ta dakatar da shirinta na gudanar da addu’a da azumi na kwanaki uku, bayan martani mai zafi daga jama’a. Tun da farko, an tsara addu’ar ne domin neman taimakon Ubangiji wajen tabbatar da tsaron (wadataccen) abinci a Nijeriya.
Wata takarda da ta bayyana ga jama’a, wadda Daraktar Gudanarwa ta Ma’aikatar, Mrs. Adedayo Modupe O., ta sanya wa hannu, ta gayyaci daraktoci da sauran manyan ma’aikata domin halartar wannan taron addu’a a shalƙwatar ma’aikatar a Abuja, a ranakun 16, 23 da 30 ga Yuni, 2025.
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025Sai dai cikin wata sabuwar sanarwa daga wannan darakta, an bayyana cewa an dakatar da shirin addu’ar har sai wani lokaci na gaba, ba tare da bayyana dalilin janye umurnin ba. Wannan matakin ya biyo bayan suka da jama’a suka yi a kafafen sada zumunta kan dacewar shirin.
Masu sukar sun bayyana cewa gwamnati ya kamata ta mai da hankali wajen samar da tsare-tsare na zahiri kamar gyaran dabarun noma, da tallafawa manoma da kuma inganta rarraba abinci, maimakon dogaro da addu’a wajen shawo kan matsalar yunwa da hauhawar farashin abinci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp