Aminiya:
2025-05-01@13:02:10 GMT

EFCC ta cafke tsohon shugaban NHIS, Usman Yusuf a Abuja

Published: 30th, January 2025 GMT

Jami’an Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC), sun cafke Tsohon Shugaban Hukumar Inshorar Lafiya ta Ƙasa (NHIS), Farfesa Usman Yusuf, bayan kai sumame a gidansa da ke Abuja.

Aminiya ta tabbatar da cewa jami’an EFCC ɗauke da makamai sun isa gidansa da misalin ƙarfe 4:46 na yammacin ranar Laraba, inda suka kama shi a gaban matarsa da ’ya’yansa.

Mutum 20 sun rasu a hatsarin jirgin sama a Sudan ta Kudu Jami’an tsaro sun mamaye sakatariyar PDP bayan ɓarkewar rikici

Sai dai har yanzu ba su bayyana dalilin cafke shi ba.

Wata majiya ta bayyana cewa an kama tare da tafiya da Farfesa Yusuf zuwa wani waje da ba a bayyana ba.

Duk da cewa hukumomi ba su fitar da sanarwa kan tuhumar da ake yi masa ba, wasu majiyoyi sun ce kamun nasa yana da alaƙa da shugabancin da ya yi a hukumar NHIS.

Wani babban jami’in EFCC ya ce, “Ba za a iya bayyana dalilin kama shi a yanzu ba saboda har yanzu ana bincike.

“Amma yana hannunmu kuma zai taimaka wajen gudanar da bincike.”

An cire Yusuf daga muƙaminsa a shekarar 2019 a lokacin mulkin tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari.

Wani kwamitin bincike na Ma’aikatar Lafiya ne, ya bayar da shawarar korarsa bisa zargin ɓatan-dabon Naira miliyan 919.

Da aka tuntuɓi kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya ce zai bincika batun sannan ya yi ƙarin haske daga baya.

Sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, bai yi martani ba.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Makiyayi Ya Kashe Abokai 2 A Nasarawa Kan Rikicin Kiwo

Michael, wanda ke zaune a Phase 4, ya yi ƙoƙarin ceton abokinsa, amma shi ma makiyayin ya sare shi da adda.

An garzaya da Michael zuwa Asibitin Mararaba domin ceto rayuwarsa, amma likita ya tabbatar da mutuwarsa bayan isar su.

‘Yansanda sun bayyana cewa an adana gawar Michael a asibitin domin gudanar da bincike.

Kwamishinan ‘yansandan jihar, ya umurci a tura jami’an tsaro domin kare rayuka da dukiya a yankin, tare da umartar Mataimakin Kwamishinan Sashen Binciken Laifuka da ya fara bincike da kuma kamo wanda ake zargi domin gurfanar da shi a kotu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ba Ya Tsoma Baki A Ayyukan EFCC – Olukoyede
  • Arif: A Shirye Muke Mu Sabunta Sana’o’in Sudan
  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  • Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APC
  • Makiyayi Ya Kashe Abokai 2 A Nasarawa Kan Rikicin Kiwo
  • Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran
  • Ƴansanda Sun Kama Ƴan Daba 33 A Kano