GORON JUMA’A 19-09-2025
Published: 19th, September 2025 GMT
Ina gaida Mahaifiyata da Mahaifina, Hajiya Saratu da Alhaji Aliyu Minjibir. Sai Gidana Alhaji Musa Yusuf, sai aminiyata Hajiya Kubra Bashir Abdullahi, sai Ƴa ta Mariya, da ƙannena Rashida Aliyu Minjibir, Zainab Aliyu Minjibir, Aliya Aliyu Minjibir, Aliyu Aliyu, Abubakar Aliyu Minjibir Muhammad Aliyu Minjibir, da fatan sun yi juma’a lafiya.
Saƙo daga Maryam M. Aminu
Saƙon gaisuwata zuwa ga Babata da Babana, sai ƙawayena kamar su; Nawal, Zee-zee Kwalale, Halima Saleh, Fatima Kabir, Maryam Isma’il (Namesake), Keleri. Sannan ƴ an’uwana Yaya, Muhammad, Iman, Al-Amin(TK), Ummulkhurthum, Jawad, Zainab Aminu, Abba, Abdulrahman, Jawahir, Fatima.
Saƙo daga Muhammad Abdullah, Unguwar Fagge Jihar Kano:
Ina gaishe da mahaifiyata da mahaifina dan ba zan fara ba sai na fara da su, sannan ina gaishe da ƴ ar’uwata rabin rai, sai abokaina, da ƴ an’uwan mahaifiyata da ƴ an’uwan mahaifina, da abokaina Aliyu, Aliyu A., Sultan, Ahmad Ghali, Amir, Iman, Ummussalama Abdulrasheed, Hajiya, Siyama, Usman Nasir, Abdulrahman Abdulrashid, Abdulsamad Abdullahi, da atan sun yi juma’a lafiya.
Saƙo daga Chef Maryam (C.E.O Meerah’s Culinary Art Bakery), daga Jihar Kano:
Saƙon gaisuwa ta musamman ga ƴ an’uwana musulmi na faɗin duniya. Sannan ina gaida iyayena sai ɗalibaina, ƙawayena da abokan aikina, kamar su; Fatima Jamilu (Nahnah’s Kitchen), Aisha Kamaluddeen (Princess Ayesha), Rukayya Muhammad Isah, Serah Johnson, Khadija Abdulhadi (Chef Dija/Dijah local Candies), Umaima Sani, Wasila Bello Umar, Dr. Hauwa Aliyu Kaita, Nr. Mrs. Fa’iza Uthman, Nafisa Omar Yahaya (Chef Omson), Dt. Maryam, Ms. Esther Samuel, Dr. Sanaya, Salma M. Rahim, Fauziyya Bukar (Fabz Delight), Asiya Khalil, Dr. Maryam A. A. Phd., Ed. Muhammad Al-amin, Kubra Auwal Yakub (African spices by Chef Hadizat), Hajiya Aisha Jabi, Halima Muhammad Dikko, Acnt. Zakiyya Habib da sauransu. Da fatan suna nan lafiya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
Sojojin Najeriya sun kashe aƙalla mayakan ƙungiyar ISWAP 8, ciki har da manyan kwamandojinta biyu a Jihar Borno.
Wata majiyar leƙen asiri daga rundunar haɗin kai ta OPHK ta bayyana cewa an kashe ’yan ta’addan ne a wata arangama da suka yi da sojojin a kan hanyar Maiduguri zuwa Baga a safiyar ranar Litinin.
DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabalaA cewar majiyoyin, an yi arangamar ce a kusa da Garin Giwa da ke gab da ƙauyen Kauwa, lokacin da ’yan ta’addan suka yi wa dakarun da ke sintiri kwanton ɓauna.
“A yayin wannan artabu, an kashe ’yan ta’adda takwas, ciki har da Munzirs biyu (kwamandojin filin daga na ƙungiyar) da kuma Qaid ɗaya (shugaban sashe).
“An kashe Modu Dogo, Munzir daga Dogon Chukun, wani Munzir da ba a bayyana ba, da Abu Aisha, shugaban sashe (Qaid) daga Tumbun Mota,” in ji wata majiya.
Majiyar ta ƙara da cewa wasu mayaƙa da dama sun samu raunuka, musamman waɗanda suka tsere da ƙafa bayan sun yi watsi da babura 14 da sojojin suka ƙwato.