Leadership News Hausa:
2025-11-03@13:08:27 GMT

GORON JUMA’A 19-09-2025

Published: 19th, September 2025 GMT

GORON JUMA’A 19-09-2025

Ina gaida Mahaifiyata da Mahaifina, Hajiya Saratu da Alhaji Aliyu Minjibir. Sai Gidana Alhaji Musa Yusuf, sai aminiyata Hajiya Kubra Bashir Abdullahi, sai Ƴa ta Mariya, da ƙannena Rashida Aliyu Minjibir, Zainab Aliyu Minjibir, Aliya Aliyu Minjibir, Aliyu Aliyu, Abubakar Aliyu Minjibir Muhammad Aliyu Minjibir, da fatan sun yi juma’a lafiya.

Saƙo daga Maryam M. Aminu 

Saƙon gaisuwata zuwa ga Babata da Babana, sai ƙawayena kamar su; Nawal, Zee-zee Kwalale, Halima Saleh, Fatima Kabir, Maryam Isma’il (Namesake), Keleri. Sannan ƴ an’uwana Yaya, Muhammad, Iman, Al-Amin(TK),  Ummulkhurthum, Jawad, Zainab Aminu, Abba, Abdulrahman, Jawahir, Fatima.

Saƙo daga Muhammad Abdullah, Unguwar Fagge Jihar Kano:

Ina gaishe da mahaifiyata da mahaifina dan ba zan fara ba sai na fara da su, sannan ina gaishe da ƴ ar’uwata rabin rai, sai abokaina, da ƴ an’uwan mahaifiyata da ƴ an’uwan mahaifina, da abokaina Aliyu, Aliyu A., Sultan, Ahmad Ghali, Amir, Iman, Ummussalama Abdulrasheed, Hajiya, Siyama, Usman Nasir, Abdulrahman Abdulrashid, Abdulsamad Abdullahi, da atan sun yi juma’a lafiya. 

Saƙo daga Chef Maryam (C.E.O Meerah’s Culinary Art Bakery), daga Jihar Kano:

Saƙon gaisuwa ta musamman ga ƴ an’uwana musulmi na faɗin duniya. Sannan ina gaida iyayena sai ɗalibaina, ƙawayena da abokan aikina, kamar su; Fatima Jamilu (Nahnah’s Kitchen), Aisha Kamaluddeen (Princess Ayesha), Rukayya Muhammad Isah, Serah Johnson, Khadija Abdulhadi (Chef Dija/Dijah local Candies), Umaima Sani, Wasila Bello Umar, Dr. Hauwa Aliyu Kaita, Nr. Mrs. Fa’iza Uthman, Nafisa Omar Yahaya (Chef Omson), Dt. Maryam, Ms. Esther Samuel, Dr. Sanaya, Salma M. Rahim, Fauziyya Bukar (Fabz Delight), Asiya Khalil, Dr. Maryam A. A. Phd., Ed. Muhammad Al-amin, Kubra Auwal Yakub (African spices by Chef Hadizat), Hajiya Aisha Jabi, Halima Muhammad Dikko, Acnt. Zakiyya Habib da sauransu. Da fatan suna nan lafiya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai

Gwamnatin Jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin fara amfani da ma’adinan ƙarƙashin ƙasa da Allah SWT ya hore ma ta da nufin haɓaka tattalin arzikinta tare da samarwa al’umma aikin yi.

A yayin ƙaddamar da taron masu ruwa da tsaki na Jihar da aka yi a babban ɗakin taron gidan gwamnatin Jihar da ke Damaturu, Gwamnan Jihar Mai Mala Buni ya ce kamfanin haɓaka ma’adanai ta Yobe Limited ita ce kawai hukumar da aka bai wa izini don gudanar da duk ayyukan bincike da haƙar ma’adinai a faɗin jihar.

Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA

Yana mai cewa, kamfanin haƙar ma’adinai na Yobe a halin yanzu shi ne, ƙashin bayan da zai samarwa Jihar hanyoyin dogaro.

“Jihar Yobe tana da wadataccen albarkatun ma’adinai kamar: Limestone, gypsum, kaolin, granite, Quartz, silica da sauran su duk da haka, tsawon shekaru da yawa, waɗannan ma’adinai sun kasance ba a amfani da su sosai kuma a yanzu lokaci ya yi da za a mayar da waɗannan ma’adinai da aka ɓoye zuwa kadarorin da za su samar da ayyukan yi, samar da wadata da kuma ciyar da ci gaban zamantakewa da tattalin arziki na mutanenmu gaba ɗaya.”

“Manufarmu ita ce tsara wani tsari don ci gaban fannin haƙar ma’adinai a Jihar Yobe ta hanyar da ta dace da manufofin Gwamnatin Tarayya na tabbatar da haɗa kan al’umma, jawo hankalin masu zuba jari masu aminci da kuma tabbatar da alhakin gyara muhalli.

“kuma mun yi imanin cewa haƙar ma’adinai idan aka sarrafa shi yadda ya kamata, zai iya zama babban abin da ke haifar da juriyar tattalin arzikin jiharmu, samar da aikin yi ga matasa da kuma samar da kuɗaɗen shiga.”

“Muna hasashen samar da fannin haƙar ma’adinai wanda zai iya aiki a cikin tsarin dokoki, wanda ke tabbatar da ɗorewar muhalli da fa’idar al’umma; wanda ke haɗaka da haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu waɗanda aka amince da riƙon amana; wanda ke jawo hankalin masu zuba jari na ƙasashen waje.” Cewar Gwamna Buni.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali
  • Allah Ya yi wa Malam Nata’ala rasuwa
  • Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai